fidelitybank

An damke Dan sandan da ya kashe abokin aikin sa a Kebbi

Date:

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kebbi, Ahmed Magaji-Kontagora, ya bayar da umarnin gudanar da bincike kan rasuwar ASP Shu’aibu Sani-Malunfashi.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan DSP Nafi’u Abubakar ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis a Birnin Kebbi.

Ya ce, a ranar 19 ga watan Oktoba, ASP Abdullahi Garba, jami’i mai kula da ofishin ‘yan sanda na Sauwa, ya samu sabani da mamacin, jami’in da ke kula da laifuka na reshen Argungu.

Kakakin ya bayyana cewa, a yayin fafatawar da suka yi a gaban shagon Garba, ya caka wa Sani-Malunfashi a haƙarƙarinsa na hagu da almakashi.

Jami’in ‘yan sandan shiyya, Argungu, ya garzaya wurin da lamarin ya faru, inda ya damke jami’in da ya aikata laifin.

DPO din ya garzaya da Sani Malunfashi asibitin Sir Yahaya Memorial da ke Birnin Kebbi, inda wani likita ya tabbatar da rasuwarsa.

A yanzu haka Abdullahi Garba na tsare a hukumar binciken manyan laifuka ta jihar (CID) dake Birnin Kebbi. An kuma mika karar zuwa sashin kisan kai.

CP Magaji-Kontagora ya aika da tawagar manyan jami’an ‘yan sanda domin ta’aziyya ga ‘yan uwa da abokanan dan sandan da ya rasu. Ya kuma roki Allah Madaukakin Sarki da ya ba shi aljanna.

legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Hisbah za ta yi wa ‘yan Daban Kano aure

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta sanar da wani...

Ganduje ya dawo Najeriya bayan ya shafe wata guda a Landan

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Ganduje,...

Barrister Sa’idu ya kama aiki bayan ya maye gurbin Muhyi Magaji

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi sabon shugaba

Farfesa Haruna Musa, ya karɓi ragamar shugabancin jami’ar Bayero...

Gwamnatin Kano ta amince Barau FC ta yi wasa a filin Sani Abacha

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kungiyar kwallon kafa...

Gwamnatin Tinubu na takalar Kwankwaso da fada – Buba Galadima

Jigo a jam'iyyar NNPP, kuma na hannun tsohon gwamnan...

Newcastle United ta dauki dan wasan tsakiya Jacob daga Aston Villa

Newcastle United ta sanar da daukar dan wasan tsakiya...

Hisba ta kama ‘yan Mata 62 da zargin aikata baɗala a Kano

Hukumar Hisbah ta kama mutane 62 kan zargin aikata...
X whatsapp