fidelitybank

An dakatar da yar damben Najeriya a gasar Olympicss

Date:

An dakatar da yar wasan damben Najeriya, Cynthia Ogunsemilor daga gasar Olympics bayan da ta gaza tsallake gwajin shan ƙwayar ƙara kuzari.

Gwajin da aka yi wa Ogunsemilor, wadda ta samu lambar yabo ta zinare a wasan Africa Games a birnin Accra a farkon shekarar nan da kuma tagulla a gasar commonwealth a Birmingham, ya nuna tana shan furosemide, ƙwayar da aka haramta sha.

Hukumar da ke bincike kan amfani da ƙwayoyin ƙara kuzari tsakanin ƴan wasan motsa jiki ce ta yi gwajin a ranar 25 ga watan Yuli a madadin kwamitin shirya gasar Olympics.

Ƴar wasan mai shekara 22 na da damar ƙalubalantar sakamakon sai dai duk wani mataki ba zai zo kan lokaci ba a abin da ka iya zama farkon wasanta a gasar Olympics a karawarta da Shih Yi Wu ta China a ranar Litinin na ajin masu nauyin kilo 60.

BBC ta tuntuɓi kwamitin shirya wasannin Olympics na Najeriya amma ba su ce komai ba.

Sakamakon Ogunsemilor na nufin yanzu Najeriya tana da ƴan wasan da aka dakatar saboda karya dokokin da suka shafi shan ƙwayoyin ƙara kuzari a wasan Olympics biyu jere bayan Blessing Okagbare da aka dakatar shekara uku da ta gabata a Tokyo.

Daga bisani an dakatar da Okagbare tsawon shekara 11 saboda amfani da wani sinadarin ƙara kuzari.

Akwai fargabar da ake cewa ba lalle bane a ƙyale yan wasan Najeriya su yi wasa a ƙarƙashin tutarsu saboda zarge-zargen hukumar da ke yaƙi da shan ƙwaya a wasanni cewa irin wannan hukumar da ke ƙasar ba ta mutunta dokokinta.

Kwamitin yaƙi da shan ƙwaya a wasanni na Najeriya ya musanta zarge-zargen kuma kotun sauraron ƙararrakin wasanni na kan bincike.

nigerianewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp