fidelitybank

An dakatar da ‘yan majalisu ba tare da ba su albashi ba a Afrika ta Kudu

Date:

An dakatar da jagoran ‘yan adawa a Afrika ta Kudu, Julius Malema tare da wadansu ‘yan majalisar dokokin su biyar na jam’iyyar EFF na tsawon wata guda ba tare da albashi ba.

Kwamitin da’a na majalisar ya same su da laifin saɓa dokokin majalisa lokacin da suka jawo tsaiko a cikin watan Fabarairu lokacin da Shugaba Cyril Ramaphosa ke jawabi a majalisa.

A wancan lokacin kakakin majalisar ya bai wa jami’an tsaro umurnin su fitar da Mista Malema daga zauren majalisar.

Kwamitin na da’a ya kuma umurci ‘yan majalisar da aka dakatar su “nemi afuwar shugaban majalisar dokoki da kuma al’ummar Afrika ta Kudu saboda matsalar da suka jawo a lokacin da shugaban kasar ya ke jawabi”.

‘Yan majalisar da aka dakatar su shida, ba za su halarci zaman majalisar ba a cikin watan Fabarairu lokacin da shugaba Ramaphosa zai yi jawabinsa na gaba a zauren.

A ranar Litinin, ‘yan majalisar na jam’iyyar EFF sun ki amincewa su bayyana gaban kwamitin da’a inda Mr Malema ya nuna rashin adawarsa a fili.

“Ba zan bayyana gaban wani bature ba,” in ji Malema.

vanguard news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp