fidelitybank

An dakatar da wasu jami’an lafiya da ake zargi da lalata marasa lafiya tare da wasu jami’an tsaron asibiti a Kano

Date:

Hakan na kunshe ne ta cikin wata Sanarwa da jami’ar yada labarai ta Hukumar kula Da Asibitocin Jihar Kano Samira Sulaiman ta raba wa manema labarai.

Sanarwar ta kara da cewa, wannan na zuwa ne ya biyo bayan wani faifan bidiyo na wata mata mai nakuda wadda daga baya ta haihu a cikin mota sakamakon sakacin da jami’an tsaron ke yi na kulawa da marasa lafiya.

A cikin wani faifan bidiyo da ya yadu hankali a kafafan sada zumunta, an gano wani mijin majinyacin ya yi ta kwankwasa kofar asibitin ba kakkautawa, amma jami’an tsaro ba kowa cikinsu, wanda hakan ya sa mijin ya dauki hoton bidiyon faruwar lamarin ya kuma tura shi kafar sada zumunta.

Dakta Nagoda ya bayyana cewa, irin wannan lamari ya taba faruwa a ranar 26 ga watan Nuwamba, inda wata mata ta na nakuda, kuma jami’an tsaron nan ma basa nan, don haka sai mijin ya garzaya da ita asibitin kwararru na Murtala Muhammad. wanda shine mafi kusa da shi a lokacin.

Haka zalika Dr Nagoda ya amince da dakatar da wasu jami’an gwaje-gwaje su uku nan take, saboda laifukan da suka hada da sakaci, karbar kudi da kuma lalata da marasa lafiya musamman wadanda suke bukatar gwajin kuma basu da kudin biyan.

Ya bayyana cewa dakatarwar ta su ya zama dole kuma za a kafa kwamitin da zai gudanar da bincike, bin hanyoyin da suka dace, duk kuma wadanda ke da hannu a ciki za a dauki mataki kansa.

Dakta Nagoda ya koka da cewa Hukumar kula da Asibitocin Jihar Kano, ba za ta kasance a bangaren tsaro a kowane lokaci ba, ya kuma yi gargadi mai karfi ga duk wanda ya ce, “Kada wanda ya isa ya zo wurina ko wasu shugabannin hukumomi su yi ta roko, tabbas ba zan dauki sakaci ba saboda mutuncinmu yana cikin hadari. “.

Sakataren zartarwa ya ci gaba da bayanin cewa jama’a da Hukumar kula Da Asibitocin Jihar Kano ya kamata su sani cewa muna da tsarin tsaro na cikin gida don tantance kwarewar mu na asibiti da kuma da’a ta kwararru.

daily post today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp