fidelitybank

An dage tashin jirgin farko na maniyatan jihar Kwara

Date:

Jirgin na farko daga filin jirgin sama na Janar Tunde Idiagbon da ke Ilorin don gudanar da aikin hajjin bana na shekarar 2024 ya koma Talata 21 ga watan Mayu.

Hukumar Alhazai ta jihar Kwara ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da babban sakataren zartarwa Abdulkadir Abdulsala ya fitar a garin Ilorin a ranar Lahadin da ta gabata, inda ya ce an samu canjin ranar daga NAHCON da kamfanonin jiragen sama sakamakon wasu tsaikon da aka samu a shirin farko.

Alhazan jihar Kwara da farko an shirya yin jigilarsu na farko a ranar Litinin 20 ga Mayu, 2024.

“Abin da wannan canjin ke nufi shi ne kada alhazanmu su sake zuwa sansanin a yau (Lahadi) kamar yadda aka sanar a baya. Su zo gobe litinin 20 ga watan Mayu, gabanin kaddamar da jirgin nasu ranar Talata da karfe 10:20 na safe.

“Wannan ya shafi mahajjata ne kawai wadanda aka shirya sunayensu a farkon tashin jirgin. Za a fitar da ƙarin bayani don shiryar da dukkan alhazanmu da sauran jama’a. Yayin da ake nadama kan wannan dan canji, amma kwata-kwata ya fita daga hannun hukumar alhazai ta jiha ko kuma wata karamar hukuma,” in ji sanarwar.

nigerian news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp