fidelitybank

An dage shari’ar Faston da ya ke rike Bindiga a Coci

Date:

A ranar Laraba ne wata kotun majistare da ke zamanta a garin Zuba da ke wajen birnin tarayya Abuja, ta dage shari’ar wani malamin Coci mai suna Uche Aigbe.

An kama Fasto na House on The Rock (HOTR), The Refuge, a Wuye, Abuja, a watan Fabrairu bisa zargin mallakar makami ba bisa ka’ida ba.

Kotun ta dage sauraren karar ne biyo bayan sauya wakilin lauyan Aigbe, Uche Uzukwu, a cewar PRNigeria.

Sabon Lauyan, Barista O. E. Ube na P. H. Ogbole SAN & Co, ya yi wannan bukata ne bisa ga sashe na 36 (A) na kundin tsarin mulkin kasar na 1999.

Lauyan masu gabatar da kara, J.C.A. Idachaba ya bayyana cewa sashe na 36 da abokin aikin sa ya ambata bai yi la’akari da yadda ake yin kasa a gwiwa ba, yana korafin aikace-aikacen tsaro suna da yawa.

Bayan sauraron muhawarar bangarorin biyu, Alkalin kotun, Abdulaziz Ismail ya dage karar zuwa ranar 25 ga watan Mayu domin sauraren karar.

Rundunar ‘yan sandan ta gurfanar da Aigbe, Promise Ukachukwu da Olakunle Ogunleye da laifin hada baki, mallakar haramtacciyar bindiga, tayar da hankali, da kuma tsoratarwa.

Hukumar tsaron ta ce wadanda ake tuhumar, dukkansu ‘yan House on The Rock, The Refuge, sun hada baki ne da mallakar bindiga kirar AK-47 ba bisa ka’ida ba a ranar 12 ga Fabrairu, 2023.

Dan sanda mai shigar da kara, Idachaba, ya shaida wa kotun cewa wadanda ake tuhumar sun samu bindiga ne daga hannun Insifekta Musa Audu wanda ke aikin gadi a Cocin.

Mataimakin Kwamishinan ‘yan sandan ya kara da cewa sun yi amfani da bindigar ne wajen wani misali a lokacin da suke wa’azi kan imani.

Rundunar ‘yan sandan ta yi zargin cewa wadanda ake tuhumar sun yi kalaman tunzura jama’a da kuma tsoratarwa ga jama’a wadanda ka iya haifar da firgici da rashin zaman lafiya.

Laifin ya ci karo da Sashe na III na Dokar Makamai CAP F28, LFN 2004, kuma ya ci karo da sashe na 97, 114, da 397 na kundin hukunta manyan laifuka.

vanguardnewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp