fidelitybank

An daƙume ɗan shekara 10 da ya tuƙa mota

Date:

Yan sanda a jihar Florida da ke Amurka, sun yi matukar kaɗuwa lokacin da suka gano cewa direban wata mota da suka tsayar a kan babbar hanya, ya kasance yaro ɗan shekara goma.

An tare yaron da ‘yar uwarsa ‘yar shekara 11 a garin Alachua da ke da nisan mil kaɗan daga inda mahaifiyarsu ta ce sun ɓace a farkon makon nan.

Ƴan sandan sun ce yaran sun tsere daga gida ne bayan da mahaifiyarsu ta ƙwace musu wayoyi.

“Mun ji mamaki da muka ga ɗan shekara goma ne yake tuka mota tare da ‘yar uwarsa,” in ji ƴan sandan.

‘Yan sanda sun kara da cewa babu wata alama da za ta nuna cewa ana cin zarafinsu a gida.

Tuni dai mahaifiyar yaran ta je garin Alachua domin kaɓar ‘ya’yanta.

Doka a Florida ta tanadi cewa sai yaro ya kai shekara 15 kafin ya iya samun izinin koyon mota, yayin da kuma sai ya kai shekara 18 kafin ya iya samun lasisin tuki. In ji BBC.

spw

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...
X whatsapp