fidelitybank

An ciro sunƙin hodar iblis 57 a cikin wani mutum ta hanyar tiyata

Date:

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi a Najeriya NDLEA ta ce an yi wa wani mutum mai shekara 59 tiyata domin ciro sunƙin hodar ibilis 57 cikin guda 81 da ya haɗiye kwanaki bakwai da suka gabata a Addis Ababa da ke Habasha.

A cikin wata sanarwa da kakakin hukumar, Femi Babafemi ya fitar, an kama mutumin ne a lokacin da ake tantance fasinjoji bayan isar su filin jirgin sama na Murtala Muhammad daga Habasha a ranar 26 ga watan da ya gabata.

Kakakin hukumar ya ce bincike ya gano cewa mutumin wanda ya yi iƙirarin ɗan kasuwa ne a yankin Oshodi da ke jihar Lagos, ya tafi Addis Ababa inda ya haɗiyi sunƙi 81 na hodar ibilis ɗin, daga bisani kuma ya hau jirgi zuwa Beirut da ke Lebanon domin kaiwa a kan kuɗi dala 3,000.

Ya kuma ce binciken nasu ya nuna cewa mutumin bai samu shiga ƙasar ba saboda kuɗin hannunsa ba su kai dala 2,000 ba da ake buƙata kafin shiga ƙasar wanda ya sa aka mayar da shi Addis Ababa inda ya yi yunƙirin fitar da miyagun ƙwayoyin amma ya kasa, daga nan kuma ya dawo Najeriya inda suka yi nasarar cafke shi.

Femi ya ƙara da cewa bayan kwanaki 5 ƙarƙashin sa idon hukumar a asibitin koyarwa na Jami’ar Jihar Lagos, mutumin ya yi kashin sunƙin hodar ibilis guda 24, inda daga bisani saboda gujewa kamuwa da rashin lafiya, aka yi masa tiyata domin cire sunƙi 57 da suka rage bayan uwargidansa da ɗan’uwansa sun amince da yin hakan.

besda salary

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp