Jamiyyar PDP mai hammaya a jihar Gombe, ta ce, wasu da ake zargim yan bangar siyasa sun cinna wuta a ofishin yakin neman zaben dan takararta na gwamnan jihar Mohamed Barde da tsakar daren jiya Litinin.
PDP ta kuma ce wannan ba shi ne karon farko da ake kai wa ofishinta hari ba.
Sai dai rundunar ‘yan sandan jihar Gombe ta ce ta soma gudanar da bincike a kan lamarin.
Babu dai cikakkun bayanai kan harin, amma dai PDP ta zargi APC da wannan hari.
A sanarwar da ta fitar, Mohammed Barde ya ce sun tafka asara sosai a harin.
Sai dai babban jami’in yada labaran gwamna mai ci Inuwa Yahaya, ya ce PDP kawai na neman abin tallata kansu ne.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan Gombe, ASP Mahid Mu’azu Abubakar, ya ce sun kaddamar da bincike kan lamarin.