fidelitybank

An ci tarar makarantar da ta wallafa hotunan dalibanta a shafin Facebook

Date:

Hukumar kula da sadarwar zamani ta Kenya ta ci tarar wata makaranta kuɗi dalar Amurka 25,000 saboda wallafa hotunan ɗalibanta a shafin intanet ba tare da samun izinin iyaye ba.

Wannan ne mataki irin haka na farko da ofishin kare bayanai ta intanet na ƙasar ya ɗauka.

Haka nan an kuma ci tarar wani gidan rawa da kuma wani kamfanin bayar da rance.

Hukumar ta ce an ci tarar gidan rawar ne bayan ya wallafa hoton wani abokin hulɗarsa a shafinsa na sada zumunta ba tare da izinin mutumin ba.

Shi kuma kamfanin bayar da rancen ya yi wa abokan hulɗarsa barazana ta hanyar kiran waya da kuma tura wa na kusa da su sakonni.

Wannan tara dai ta haifar da muhawara a ƙasar game da sirrin bayanan al’umma da kuma yadda kamfanoni ke amfani da su.

A wani saƙo da hukumar ta wallafa a shafinta na X, ta ce tana sa ran wannan tara za ta zama izina da kamfanoni domin su riƙa martaba dokokin kare bayanan al’umma, ciki har da batun neman izinin mutane kafin wallafa hotunansu a shafukan intanet.

nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp