Hukumar kula da sadarwar zamani ta Kenya ta ci tarar wata makaranta kuɗi dalar Amurka 25,000 saboda wallafa hotunan ɗalibanta a shafin intanet ba tare da samun izinin iyaye ba.
Wannan ne mataki irin haka na farko da ofishin kare bayanai ta intanet na ƙasar ya ɗauka.
Haka nan an kuma ci tarar wani gidan rawa da kuma wani kamfanin bayar da rance.
Hukumar ta ce an ci tarar gidan rawar ne bayan ya wallafa hoton wani abokin hulɗarsa a shafinsa na sada zumunta ba tare da izinin mutumin ba.
Shi kuma kamfanin bayar da rancen ya yi wa abokan hulɗarsa barazana ta hanyar kiran waya da kuma tura wa na kusa da su sakonni.
Wannan tara dai ta haifar da muhawara a ƙasar game da sirrin bayanan al’umma da kuma yadda kamfanoni ke amfani da su.
A wani saƙo da hukumar ta wallafa a shafinta na X, ta ce tana sa ran wannan tara za ta zama izina da kamfanoni domin su riƙa martaba dokokin kare bayanan al’umma, ciki har da batun neman izinin mutane kafin wallafa hotunansu a shafukan intanet.