Firaministan Biritaniya, Boris Johnson da Ministan Kudi Rishi Sunak na shirin biyan tara, saboda keta ka’idojin kullen korona.
‘Yan sanda sun gudanar da bincike kan wasu tarukan holewa 12 da ake zargin sun halarta, kuma an gano cewa Mista Johnson ya halarci akalla uku daga cikinsu.
A wani taron da aka yi a ofishin majalisar ministoci an gabatar masa da kek na murnar zagayowar ranar haihuwarsa.
Zuwa yanzu ofishin ‘yan sandan kwaryar birnin Landan ya ci tarar sama da mutane 50 saboda halartar tarukan a gine-ginen da aka sanya dokar korona, kuma fadar mulki ta Downing ta ce za ta tabbatar ko Mista Johnson na cikinsu.
Shugaban jam’iyyar Labour, Keir Starmer, ya ce dole ne Firaministan da ministansa su yi murabus saboda yadda mai dokar bacci ya bide da gyangyadi.