fidelitybank

An ceto ƴan Najeriya 58 da aka yi safarar su zuwa Ghana

Date:

Hukumar da ke kula da ƴan Najeriya a ƙasashen waje, NIDCOM ta ce ta ceto mata da ƙananan yara 58 daga hannun masu safarar mutane a Ghana.

Shugabar NDICOM, Abike Dabiri-Erewa ta ce wannan na zuwa ne bayan hukumar ta samu nasarar kuɓutar da wata yarinya ƴar mai shekara 15 zuwa 16 daga hannun masu neman yin safarar ta.

Sanarwar da kakakin hukumar, Abdur-Rahman Balogun ya fitar ta ce Abike Dabiri-Erewa ta samu labarin ceto ƴan Najeriyar daga Ghana ne a lokacin da ta kai ziyara domin ganin mutanen da aka yi safara zuwa birnin Accra na ƙasar Ghana.

Sanarwar ta ce daga cikin wadanda aka ceto akwai 47 ƴan asalin jihar Kano da biyar daga Katsina da biyu daga Jigawa da kuma huɗu daga jihar Kaduna.

Balogun ya bayyana cewa a cikin wata uku jimillar ƴan Najeriya 105 kenan da aka samu nasarar ceto su daga hannun masu safara a birnin Accra.

Hukumar ta ce, ta riga ta mayar da zangon farko na mutanen ceto zuwa gida Najeriya.

Ta kuma bayyana cewa, mafi yawan waɗanda ake safarar suna faɗawa tarko ne a bisa alƙawarin za a samar masu aiki a ƙasashen waje, wanda kuma hanya ce kawai ta yaudara ba gaskiya ba.

nigerianewspapers.com.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...
X whatsapp