Ana ci gaba da samun labarai da hotuna marassa daɗi game da bala’in girgizar ƙasar da ya afka wa Turkiyya da Syria.
A birnin Hayat, na Turkiyya an zaƙulo wani ƙaramin yaro mai shekara takwas daga cikin ɓaraguzan ginin da ya faɗi bayan sa’o’i 52.
An ceto Yigit Cakmak a gaban mahaifiyarsa, wadda ta rungume shi bayan an fito da shi.
Karanta Wannan: An ceto mutane 24 da ginin Abuja ya danne su
Zuwa yanzu ana ganin wadanda suka mutu a sanadiyyar girgizar kasar da ta auku ranar Litinin a Turkiyya da Syria sun wuce dubu 11.
Hukumomin Turkiyya sun ce zuwa lokacin wannan rahoto mutum 8,574 suka rasa ransu a kasar.
Abu ne mai wuya a samu alkaluma daga Syria, amma muna ganin yawan wadanda suka rasun zuwa yanzu sun kai 2,662.