fidelitybank

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Date:

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami’anta sun samu nasarar ceto yara 12 da aka yi safararsu a Jihar Abia tare da ƙwato makamai da alburusai da dama a Jihar Kogi.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar a shafin sada zumuntarta na X.

“A Jihar Abia, jami’anmu sun kama mutum biyu bisa zargin gudanar da gidan yara marayu ba bisa ƙa’ida ba a cikin gidansu dake kan titin Ikot Ekpene, Aba inda aka gano yara 12 daga tsakanin watanni shida zuwa shekaru 14 a cikin gidan.” in ji sanarwar

Bincike dai ya nuna cewa an yi safarar yaran ne daga ƙauyuka daban-daban a yankin Arochukwu.

“An miƙa yaran da aka ceto ga ma’aikatar harkokin mata ta Jihar Abia domin kula da su.” sanarwar ta ƙara da cewa.

“Masu laifin kuma na hannun hukuma suna fuskantar tambayoyi, kuma za a gurfanar da su a kotu bayan kammala bincike.” rundunar ta ƙar da cewa.

A wani samame kuma ta daban a Jihar Kogi, jami’an ‘yan sanda sun ce sun daƙile wata mota ɗauke da makama da alburusai da dama.

“Ana zargin wannan makamai da alaka da wani fashi da makami da aka yi kwanan nan a wajen saida man fetur a Kabba.” in ji sanarwa.

Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, IGP Kayode Egbetokun ya buƙaci ‘yan Najeriya da su ci gaba da kasancewa masu lura da tsaro, kada su ba yara ga mutanen da ba su sani ba, tare da gaggauta kai rahoton duk wata motsi ko mutum da ake zargi zuwa ofishin ‘yan sanda mafi kusa.

mmm.nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp