Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami’anta sun samu nasarar ceto yara 12 da aka yi safararsu a Jihar Abia tare da ƙwato makamai da alburusai da dama a Jihar Kogi.
Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar a shafin sada zumuntarta na X.
“A Jihar Abia, jami’anmu sun kama mutum biyu bisa zargin gudanar da gidan yara marayu ba bisa ƙa’ida ba a cikin gidansu dake kan titin Ikot Ekpene, Aba inda aka gano yara 12 daga tsakanin watanni shida zuwa shekaru 14 a cikin gidan.” in ji sanarwar
Bincike dai ya nuna cewa an yi safarar yaran ne daga ƙauyuka daban-daban a yankin Arochukwu.
“An miƙa yaran da aka ceto ga ma’aikatar harkokin mata ta Jihar Abia domin kula da su.” sanarwar ta ƙara da cewa.
“Masu laifin kuma na hannun hukuma suna fuskantar tambayoyi, kuma za a gurfanar da su a kotu bayan kammala bincike.” rundunar ta ƙar da cewa.
A wani samame kuma ta daban a Jihar Kogi, jami’an ‘yan sanda sun ce sun daƙile wata mota ɗauke da makama da alburusai da dama.
“Ana zargin wannan makamai da alaka da wani fashi da makami da aka yi kwanan nan a wajen saida man fetur a Kabba.” in ji sanarwa.
Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, IGP Kayode Egbetokun ya buƙaci ‘yan Najeriya da su ci gaba da kasancewa masu lura da tsaro, kada su ba yara ga mutanen da ba su sani ba, tare da gaggauta kai rahoton duk wata motsi ko mutum da ake zargi zuwa ofishin ‘yan sanda mafi kusa.