fidelitybank

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Date:

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami’anta sun samu nasarar ceto yara 12 da aka yi safararsu a Jihar Abia tare da ƙwato makamai da alburusai da dama a Jihar Kogi.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar a shafin sada zumuntarta na X.

“A Jihar Abia, jami’anmu sun kama mutum biyu bisa zargin gudanar da gidan yara marayu ba bisa ƙa’ida ba a cikin gidansu dake kan titin Ikot Ekpene, Aba inda aka gano yara 12 daga tsakanin watanni shida zuwa shekaru 14 a cikin gidan.” in ji sanarwar

Bincike dai ya nuna cewa an yi safarar yaran ne daga ƙauyuka daban-daban a yankin Arochukwu.

“An miƙa yaran da aka ceto ga ma’aikatar harkokin mata ta Jihar Abia domin kula da su.” sanarwar ta ƙara da cewa.

“Masu laifin kuma na hannun hukuma suna fuskantar tambayoyi, kuma za a gurfanar da su a kotu bayan kammala bincike.” rundunar ta ƙar da cewa.

A wani samame kuma ta daban a Jihar Kogi, jami’an ‘yan sanda sun ce sun daƙile wata mota ɗauke da makama da alburusai da dama.

“Ana zargin wannan makamai da alaka da wani fashi da makami da aka yi kwanan nan a wajen saida man fetur a Kabba.” in ji sanarwa.

Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, IGP Kayode Egbetokun ya buƙaci ‘yan Najeriya da su ci gaba da kasancewa masu lura da tsaro, kada su ba yara ga mutanen da ba su sani ba, tare da gaggauta kai rahoton duk wata motsi ko mutum da ake zargi zuwa ofishin ‘yan sanda mafi kusa.

the punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Yansanda sun kama Sojoji cikin ‘ƴan ƙungiyar asiri’ a jihar Ogun

Rundunar 'yansanda reshen jihar Ogun, ta tabbatar da kama...

Yadda ambaliya ta shanye Adamawa

Rahotonni daga birnin Yola na jihar Adamawa na cewa,...

Yadda Jodan da Dubai ke jefa wa al’ummar Gaza abinci ta sama

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Jordan ta ce, jiragen...

Tarihi ba zai manta da Najeriya ba a bangaren kwallon kafar Mata

Najeriya ta lashe kofin ƙwallon Afirka na mata karo...

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar ɗan wasan...

Sojoji sun kashe rikaken dan Bindiga Dan Dari Biyar a Sokoto

Dakarun Operation FANSAR YANMA sun yi nasarar fatattakar wani...

An kashe utane 30 a yakin Thailand da Cambodia

An shiga kwana na uku na faɗan kan iyaka...

Ba mu ƙayyade shekarun shiga ƙaramar sakandare JSS1 – Ma’aikatar Ilimi

Ma'aikatar Ilimi a Najeriya ta musanta rahoton da wasu...

Ido da Ido na ga yadda Sojojin Isra’ila ke kashe Falasdinawa – Tsohon Sojin Amurka

Wani tsohon sojan Amurk ya ce, ya ga yadda...

‘Yan majalisar Birtaniya 220 na neman ƙasar ta amice da ƙasar Falasɗinu

'Yan majalisar Birtaniya 220 sun nemi gwamnatin ƙasar ta...

Buhari yaki karbar kyautar Agogon lu’u-lu’u da jirgin sama – Garba Shehu

Mai magana da yawun tsohon Shugaban Najeriya Muhammad Buhari,...

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...
X whatsapp