fidelitybank

An ceto Yara 10 daga safarar mutane a Kano

Date:

Hukumar dake Yaki da Safarar Mutane ta kasa (NAPTIP), reshen Kano, ta karbi wasu mutum 10 da aka ceto daga hannun masu safarar mutane.

Shugaban hukumar, Abdullahi Babale ne ya bayyana haka a Alhamis din nan a Kano, yayin da ya karbi wadanda aka ceto daga hannun Rundunar ‘Yan Sanda.

A cewarsa, an ceto wadanda aka yi safara ne a ranar 7 ga Disamba da misalin karfe 2:40 na yamma a wani gida da ke Unguwar Rijiyar Lemo, a wani samame da wata tawagar ‘yan sanda karkashin jagorancin CSP Bala Shuaibu suka kai yankin.

Babale ya kara da cewa, wadanda aka ceto, wanda shekarunsu ke tsakanin 22 zuwa 42, sun hada da mata 6 da maza 4, yana mai bayyana cewa “suna kan hanyarsu ta zuwa Libiya domin aikatau.”

Shugaban ya kuma yaba da taimako da hadin kan kwamishinan ‘yan sandan Jihar Kano, Salman Dogo Garba kan wannan yunkuri.

A nasa bangaren, kwamsihinan ‘yan sanda ya ce, “Za a ba wa wadanda aka ceto shawarwari yadda zasu gyaran halayensu kafin mayar da su ga iyalansu.”

Ya kuma yi kira ga iyaye da su kare ‘ya’yansu daga fadawa hannun masu safara da kan jefa su cikin bauta da sunan neman sabuwar rayuwa.

bbc news nigeria today live

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp