fidelitybank

An ceto Uwa da ‘ya a karkashin kasa bayan kwana biyar a Turkiyya

Date:

Duk da raguwar fatan da ake da shi na samun mutanen da suka maƙale a cikin ɓaraguzan ginin da ransu, ana ci gaba da samun abubuwa na ban al’ajabi a yankin da ake ceton waɗanda girgizar ƙasar ta rutsa da su.

Kwanaki biyar tun bayan afkuwar mummunan bala’in girgizar ƙasa da ya kai maki 7.8 a Turkiyya, har yanzu ana ci gaba da zaƙulo mutane da ransu daga cikin ɓaraguzan gini.

Wani bidiyo da aka wallafa a shafukan sada zumunta a ƙasar ya nuna lokacin da aka ceto wata mace mai ciki tare da ƙaramar ‘yarta daga cikin wani gini da ya ruguje a birnin Gaziantep na Turkiyya bayan kwashe sa’o’i 115 maƙale cikin ginin.

An dai samu rahotonnin kuɓutar da wasu mutane ciki har da wani matashi, a wasu yankunan Turkiyya bayan sa’o’i 110 maƙale cikin ɓaraguzai.

Wani bidiyo da tawagar ceto ta Jamus ta fitar ya nuna yadda aka zaƙulo wata yarinya da ranta ƙarƙashin ɓaraguzai a birnin Kahramanmaras bayan kwashe sama da sa’o’i 110.

Haka kuma hukumar jin kai ta Turkiyya ta saki bidiyon wani mutum cikin motar ɗaukar marasa lafiya, da ta kuɓutar da ransa a kusa da Kahramanmaras. In ji BBC.

latest news 
in nigeria today 2021 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp