fidelitybank

An ceto mutanen da aka sace bayan an yi wa ayarin ofishin Amurka kwantan bauna

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Anambra, ta ceto mutanen da aka sace bayan da aka yi wa ayarin ofishin Amurka kwanton bauna.

Jami’in hulda da jama’a, DSP Ikenga Tochukwu ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar da safiyar Juma’a.

“Da sanyin safiyar yau 19/5/2023, jami’an tsaro na hadin gwiwar sun ceto biyun da aka yi garkuwa da su.

Karanta Wannan: Zamu taimakawa Najeriya wajen gano wanda suka kashe ma’aikatan mu – Amurka

An cafke mutane biyu da ake zargi da kashe jami’an jakadancin Amurka

Kakakin ya kara da cewa “har yanzu ana ci gaba da wuraren da kuma za a yi karin bayani.”

An kai harin ne a ranar 16 ga watan Mayu a kan hanyar Atani/Osamela a karamar hukumar Ogbaru (LGA) ta jihar Anambra.

Tawagar ta Amurka da ta hada da jami’an Najeriya da na Amurka, sun yi wani aiki ne na kawo illar zaizayar kasa a karamar hukumar Ogbaru.

Rundunar ‘yan sandan ta ce mutane tara ne suka mutu tare da dora laifin a kan ‘yan kungiyar ‘yan asalin yankin Biafra (IPOB).

Sunan su Jefferson Obayuwane (ma’aikacin DSS mai ritaya), Sunday Prince Ubong, Ekene Nweke, Hassan Etila, Avwuvie Kaye.

Sauran wadanda suka rasa rayukansu akwai ‘yan sanda hudu: Bukar A. Kabuiki, Emmanuel Lukkpata, Friday Morgan da Adamu Andrew.

Rundunar ‘yan sanda ta tabbatar da cewa an tsinto gawarwakin wadanda suka mutu kuma an ajiye su a dakin ajiyar gawa.

bbc nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp