Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Katsina, sun ceto mutane akalla 30 da aka yi garkuwa da su tare da dakile hare-haren ‘yan bindiga da dama a wasu hare-hare da suka kai a fadin jihar.
Lamarin na baya-bayan nan ya faru ne a ranar 21 ga watan Agusta lokacin da DPO na rundunar ‘yan sandan Dutsinma, CSP Bello Abdullahi Gusau ya jagoranci tawagar ‘yan sanda da ‘yan banga tare da kai samame a maboyar ‘yan bindiga a karamar hukumar Dutsinma.
An ce an kubutar da wasu mutane bakwai da aka yi garkuwa da su a kauyukan Farar Kasa da Shanga da ke karamar hukumar Dutsinma ba tare da sun ji rauni ba, sannan kuma an samu nasarar kwato bindiga kirar AK47 guda daya a yayin farmakin.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Aliyu Abubakar Musa, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar, ASP Abubakar Sadiq ya sanyawa hannu a ranar Alhamis.
CP Musa ya ci gaba da bayyana cewa, bayan wani kazamin fadan da aka yi a wasu wurare daban-daban a wannan rana, jami’an ‘yan sanda sun dakile harin ‘yan bindiga a Malumfashi da karamar hukumar Jibia, inda suka ceto mutane 20 da aka yi garkuwa da su da kuma shanu biyar da aka yi garkuwa da su a kauyen Yaba da ke Malumfashi.
Yayin da suke Jibia, rundunar ta ceto mutane uku da aka yi garkuwa da su daga hannun ‘yan bindiga da suka kai hari kauyukan Jibian Maje, Nasarawa, da kuma Lankwasau.
CP Musa ya yabawa bajintar jami’an ‘yan sandan da suka yi aikin. Ya bukaci jama’a da su ci gaba da tallafa wa ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro da bayanai kan lokaci don taimakawa wajen yaki da miyagun laifuka a jihar.