fidelitybank

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

Date:

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale da ya afku a jihar Sokoto, a cewar ɗan majalisar wakilai daga mazaɓar Goronyo/Gada na jihar, Bashir Gorau.

Ya ce ana fargabar akwai mutum 40 da suka ɓace kawo yanzu bayan da kwale-kwalen ɗauke da fasinjoji sama da 50 ya kife ranar Lahadi.

“Zuwa yanzu muna ci gaba da bibiyar lamarin, sannan akwai mutanen mu da suka iya ruwa da ke ƙoƙari wajen ganin sun cigaba da ceto sauran mutane. Mun ceto mutum 26 kawo yanzu,” kamar yadda ɗan majalisar ya shaida wa gidan talabijin na Channels a wata tattauna ranar Talata.

Ya kuma ce sun buƙaci hukumomin da ke kula da madatsar ruwa ta Goronyo da su rufe ruwan na tsawon kwanaki biyu don ganin ruwan ya ragu, saboda a ci gaba da aikin ceto.

Alkaluma da hukumar ba da agajin gaggawa ta ƙasa NEMA ta fitar tun da farko, sun nuna cewa ana fargabar kusan mutum 40 ne suka rasu a hatsarin.

Sai dai, Gorau ya yi imanin cewa “babu ainihin alkaluman waɗanda suka ɓace” daga wannan mummunan hatsari.

“Hasashe ne ake yi cewa mutum 40 ko 50 sun ɓace, sai dai babu takamaimen alkaluman mutanen,” in ji ɗan majalisar.

Ya kuma koka kan yadda ake yawan samun hatsarin jiragen ruwa, inda ya ɗora laifin hakan kan rashin bn matakan kariya na shiga ruwa.

cnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Barrister Sa’idu ya kama aiki bayan ya maye gurbin Muhyi Magaji

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi sabon shugaba

Farfesa Haruna Musa, ya karɓi ragamar shugabancin jami’ar Bayero...

Gwamnatin Kano ta amince Barau FC ta yi wasa a filin Sani Abacha

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kungiyar kwallon kafa...

Gwamnatin Tinubu na takalar Kwankwaso da fada – Buba Galadima

Jigo a jam'iyyar NNPP, kuma na hannun tsohon gwamnan...

Newcastle United ta dauki dan wasan tsakiya Jacob daga Aston Villa

Newcastle United ta sanar da daukar dan wasan tsakiya...

Hisba ta kama ‘yan Mata 62 da zargin aikata baɗala a Kano

Hukumar Hisbah ta kama mutane 62 kan zargin aikata...

NNPP ta yi tafka magudi a zabencike gurbin Kano – Farouk Lawan

Tsohon dan majalisar wakilai, Farouk Lawan, ya yi zargin...

Dan shugaban kungiyar Boko Haram ya shiga hannu

Hukumomi a ƙasar Chadi sun kama yaron shugaban ƙungiyar...
X whatsapp