fidelitybank

An ceto Mutane 25 da syka kife a kwale-kwalen Sokoto

Date:

Hukumomi a jihar Sokoto sun ce, sun samu nasarar ceto mutum 25 da ransu daga cikin waɗanda suka ɓace a haɗarin kwale-kwale da ya auku a ƙauyen Kojiyo da ke ƙaramar hukumar Goronyo ta jihar.

Haɗarin ya auku ne a lokacin da mutum 50 suke hanyar tafiya babbar kasuwar Goronyo da ke Sokoto, inda tun a farko aka ceto mutum 10.

Wani kansila da ke yankin ya bayyana wa BBC cewa har yanzu ana neman sauran mutum 25.

“Mutum 50 ne a kwale-kwalen da babura 7 da wasu buhunan kayan abinci. An ceto mutum 25 zuwa yanzu, sannan ana ci gaba da neman sauran 25 ɗin,” in ji Aminu Bare.

Shugaban hukumar agajin gaggawa ta jihar Sokoto, Aminu Liman ya shaida wa BBC cewa an tura ƙwararrun masu aikin ceto domin su higa kogin domin ceto sauran waɗanda suka rage.

thisdaynews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Logged in as Adam Ahmed. Log out?

Please enter your comment!

Share post:

Popular

More like this
Related

An ceto Mutane 25 da syka kife a kwale-kwalen Sokoto

Hukumomi a jihar Sokoto sun ce, sun samu nasarar...

An fara duba rabon gyaran arzikin Najeriya

Shugaban Hukumar rarraba arziƙin ƙasa RMAFC, Mohammed Shehu, ya...

Kwallaye 6 da aka zurawa Santos a raga ta sanya Neymar ya fashe da kuka

Ɗan wasan tawagar Brazil, Neymar ya fice daga cikin...

Hukumar Shari’a ta magantu kan sadakin dubu 20 da ya yamutsa hazo a Kano

Hukumar shari’a ta jihar Kano, ta ce ba a...

Cutar Mashako ta yi ajalin Yara hudu a Kano

Rahotanni na cewa cutar mashaƙo wadda aka fi sani...

Cin zaben da NNPP ta yi a Kano cuwa-cuwa ne – Ata

Ministan Jiha na Gidaje da Cigaban Birane, Rt Hon...

Mutane kusan 40 sun ɓace sakamakon haɗarin kwale-kwale a Sokoto

Aƙalla mutum 40 ne ake nema bayan haɗarin kwale-kwale...

APC ta yi kwaf daya a zaben cike gurbin Kaduna da Jigawa

Jam'iyyar APC mai mulki a jihar Jigawa ta yi...

Ba mu yarda da zaben Ghari da Tsanyawa ba – NNPP

Jam'iyar NNPP mai mulkin jihar Kano a arewacin Najeriya...

QPC ta nemi INEC ta soke zaɓen Kano

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe...

Zaɓen Kano: An kama Mutane 288 da tayar da zaune tsaye

Rudunar ƴansandan jihar Kano, ta sanar da kama mutum...

An Kama wakilin jam’iyya da Naira miliyan 25.9 na Siyan Kuri’a

Jami’an tsaro sun kama wani da ake zargin wakilin...
X whatsapp