fidelitybank

An ceto Jaririn da gini ya danne shi a Syria

Date:

Masu aikin agaji sun ceto wata jaririya sabuwar haihuwa daga cikin baraguzan gine-ginen da suka rushe a sakamakon girgizar kasa a yankin arewa maso yammacin Syria ranar Litinin.

mahaifiyarta ta fara nakuda ne jim kadan bayan girgizar kasar, sannan ta haihu kafin ta rasu, in ji wani danginsu.

Majiyar ta ce mahaifin yarinyar da ‘yan uwanta hudu da kuma kanwar mahaifiyarta duk sun rasu a girgizar kasar.

An wani hoton bidiyo mai cike da mamaki an ga wani mutum na rike da jaririyar wadda ta yi budu-budu da kura, bayan da aka fito da ita daga cikin buraguzai a garin Jindayris.

Wani likita a wani asibiti na kusa da garin da aka ceto ta, Afrin ya ce jaririyar a yanzu tana nan cikin kyakkyawan yanayi.

Gidan da mahaifanta suke na daya daga cikin gine-gine 50 da rahotanni suka ce girgizar kasar mai karfin maki 7.8 ta lalata a Jindayris, wanda gari ne da ke hannun ‘yan hamayya a lardin Idlib da ke kusa da iyaka da Turkiyya.

Kawun jaririyar, Khalil al-Suwadi, ya ce suna samun labarin rugujewar ginin sai suka ruga domin su ga abin da ya faru.

”Mun ji murya a lokacin da muke tona buraguzai, ” kamar yadda ya sheda wa kamfanin dillancin labarai na AFP a ranar Talata.

Karanta Wannan: An ceto yaro da ya shafe sa’o’i 52 a cikin baraguzai

”Da muka kawar da kasar sai muka samu jaririyar da mabiyiyarta, sai muka yanke mabiyiyar aka tafi da jaririyar asibiti.”

Likitan yara Hani Maarouf ya ce an kai jaririyar asibitinsa a yanayi maras kyau, saboda ta kukkuje ga kuma tsananin sanyi da ya taba ta”.

”To amma yanzu ta samu sauki,” in ji likitan.

An gudanar da jana’iza ta gaba-daya ga mahaifiyarta Afraa, da mahaifinta Abdullah da kuma ‘yan uwanta hudu.

Suna daga cikin mutane 1,800 da aka san cewa sun rasu a girgizar kasar a Syria, kamar yadda bayanai suka nuna.

legit news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...

Bajintar É—aliban Najeriya a gasar Turanci ta nuna ingancin ilimi a Æ™asa – Tinubu

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, ya taya Æ´anmatan nan uku...

Ƙudirin faÉ—aÉ—a mamayar Gaza zai Æ™ara jefa FalasÉ—inawa cikin hatsari – MDD

Majalisar ÆŠinkin Duniya ta bayyana rahotannin da ke kwarmata...

APC a Kano mu na jinjinawa Tinubu – Abdullahi Abbas

Shugabannin jam’iyyar APC a jihar Kano, sun yabawa shugaba...

Kwamishinan da ake tuhuma da belin dilan kwayoyi a Kano ya yi murabus

Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi ya...

Turji ya saki Mutane 32 bayan zaman sulhu

Shahararren shugaban ‘yan bindiga, Bello Turji, ya saki mutane...

ADC ta gargadi El’Rufa’i kan ruguza jam’iyyar

Shugaban jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a jihar Kaduna,...

An gindayawa Thomas Partey sharudan beli

An gindaya sharuddan belin tsohon dan wasan tsakiya na...

Fursunoni 37 na jiran zartas musu da hukuncin kisa a Bauchi

Fursunoni 37 da aka yanke wa hukuncin kisa bisa...

Kwamitin sulhu na MDD zai gana kan makomar Æ´an Isra’ila da ke hannun Hamas

Kwamitin tsaro na Majalisar ÆŠinkin Duniya zai tattauna yau...
X whatsapp