fidelitybank

An ceto Jaririn da gini ya danne shi a Syria

Date:

Masu aikin agaji sun ceto wata jaririya sabuwar haihuwa daga cikin baraguzan gine-ginen da suka rushe a sakamakon girgizar kasa a yankin arewa maso yammacin Syria ranar Litinin.

mahaifiyarta ta fara nakuda ne jim kadan bayan girgizar kasar, sannan ta haihu kafin ta rasu, in ji wani danginsu.

Majiyar ta ce mahaifin yarinyar da ‘yan uwanta hudu da kuma kanwar mahaifiyarta duk sun rasu a girgizar kasar.

An wani hoton bidiyo mai cike da mamaki an ga wani mutum na rike da jaririyar wadda ta yi budu-budu da kura, bayan da aka fito da ita daga cikin buraguzai a garin Jindayris.

Wani likita a wani asibiti na kusa da garin da aka ceto ta, Afrin ya ce jaririyar a yanzu tana nan cikin kyakkyawan yanayi.

Gidan da mahaifanta suke na daya daga cikin gine-gine 50 da rahotanni suka ce girgizar kasar mai karfin maki 7.8 ta lalata a Jindayris, wanda gari ne da ke hannun ‘yan hamayya a lardin Idlib da ke kusa da iyaka da Turkiyya.

Kawun jaririyar, Khalil al-Suwadi, ya ce suna samun labarin rugujewar ginin sai suka ruga domin su ga abin da ya faru.

”Mun ji murya a lokacin da muke tona buraguzai, ” kamar yadda ya sheda wa kamfanin dillancin labarai na AFP a ranar Talata.

Karanta Wannan: An ceto yaro da ya shafe sa’o’i 52 a cikin baraguzai

”Da muka kawar da kasar sai muka samu jaririyar da mabiyiyarta, sai muka yanke mabiyiyar aka tafi da jaririyar asibiti.”

Likitan yara Hani Maarouf ya ce an kai jaririyar asibitinsa a yanayi maras kyau, saboda ta kukkuje ga kuma tsananin sanyi da ya taba ta”.

”To amma yanzu ta samu sauki,” in ji likitan.

An gudanar da jana’iza ta gaba-daya ga mahaifiyarta Afraa, da mahaifinta Abdullah da kuma ‘yan uwanta hudu.

Suna daga cikin mutane 1,800 da aka san cewa sun rasu a girgizar kasar a Syria, kamar yadda bayanai suka nuna.

nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp