fidelitybank

An ceto Jaririn da gini ya danne shi a Syria

Date:

Masu aikin agaji sun ceto wata jaririya sabuwar haihuwa daga cikin baraguzan gine-ginen da suka rushe a sakamakon girgizar kasa a yankin arewa maso yammacin Syria ranar Litinin.

mahaifiyarta ta fara nakuda ne jim kadan bayan girgizar kasar, sannan ta haihu kafin ta rasu, in ji wani danginsu.

Majiyar ta ce mahaifin yarinyar da ‘yan uwanta hudu da kuma kanwar mahaifiyarta duk sun rasu a girgizar kasar.

An wani hoton bidiyo mai cike da mamaki an ga wani mutum na rike da jaririyar wadda ta yi budu-budu da kura, bayan da aka fito da ita daga cikin buraguzai a garin Jindayris.

Wani likita a wani asibiti na kusa da garin da aka ceto ta, Afrin ya ce jaririyar a yanzu tana nan cikin kyakkyawan yanayi.

Gidan da mahaifanta suke na daya daga cikin gine-gine 50 da rahotanni suka ce girgizar kasar mai karfin maki 7.8 ta lalata a Jindayris, wanda gari ne da ke hannun ‘yan hamayya a lardin Idlib da ke kusa da iyaka da Turkiyya.

Kawun jaririyar, Khalil al-Suwadi, ya ce suna samun labarin rugujewar ginin sai suka ruga domin su ga abin da ya faru.

”Mun ji murya a lokacin da muke tona buraguzai, ” kamar yadda ya sheda wa kamfanin dillancin labarai na AFP a ranar Talata.

Karanta Wannan: An ceto yaro da ya shafe sa’o’i 52 a cikin baraguzai

”Da muka kawar da kasar sai muka samu jaririyar da mabiyiyarta, sai muka yanke mabiyiyar aka tafi da jaririyar asibiti.”

Likitan yara Hani Maarouf ya ce an kai jaririyar asibitinsa a yanayi maras kyau, saboda ta kukkuje ga kuma tsananin sanyi da ya taba ta”.

”To amma yanzu ta samu sauki,” in ji likitan.

An gudanar da jana’iza ta gaba-daya ga mahaifiyarta Afraa, da mahaifinta Abdullah da kuma ‘yan uwanta hudu.

Suna daga cikin mutane 1,800 da aka san cewa sun rasu a girgizar kasar a Syria, kamar yadda bayanai suka nuna.

hausa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaÆ™i don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin Æ™era nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe Æ´an Æ™asarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faÉ—a kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta Æ™addamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo Æ™arshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar Æ´ansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin Æ´an Æ™asarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a Æ™yale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp