fidelitybank

An ceto ƴan Najeriya 58 da aka yi safarar su zuwa Ghana

Date:

Hukumar da ke kula da ƴan Najeriya a ƙasashen waje, NIDCOM ta ce ta ceto mata da ƙananan yara 58 daga hannun masu safarar mutane a Ghana.

Shugabar NDICOM, Abike Dabiri-Erewa ta ce wannan na zuwa ne bayan hukumar ta samu nasarar kuɓutar da wata yarinya ƴar mai shekara 15 zuwa 16 daga hannun masu neman yin safarar ta.

Sanarwar da kakakin hukumar, Abdur-Rahman Balogun ya fitar ta ce Abike Dabiri-Erewa ta samu labarin ceto ƴan Najeriyar daga Ghana ne a lokacin da ta kai ziyara domin ganin mutanen da aka yi safara zuwa birnin Accra na ƙasar Ghana.

Sanarwar ta ce daga cikin wadanda aka ceto akwai 47 ƴan asalin jihar Kano da biyar daga Katsina da biyu daga Jigawa da kuma huɗu daga jihar Kaduna.

Balogun ya bayyana cewa a cikin wata uku jimillar ƴan Najeriya 105 kenan da aka samu nasarar ceto su daga hannun masu safara a birnin Accra.

Hukumar ta ce, ta riga ta mayar da zangon farko na mutanen ceto zuwa gida Najeriya.

Ta kuma bayyana cewa, mafi yawan waɗanda ake safarar suna faɗawa tarko ne a bisa alƙawarin za a samar masu aiki a ƙasashen waje, wanda kuma hanya ce kawai ta yaudara ba gaskiya ba.

spw

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...

Shugaban Laberiya ya je ta’aziyyar Buhari a Monrovia

Shugaban Ƙsaar Laberiya Joseph Nyuma Boakai ya kai ziyarar...

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...

Iran ta zartar da hukuncin kisa a kan Mutane 3

Hukumomi a Iran sun zartar wa mutum uku hukuncin...

Ƴansanda sun kama ƙasurgumin ɗanbindiga a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna ta ce, jami'an ta sun...

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...
X whatsapp