fidelitybank

An ceto ƴan Najeriya 58 da aka yi safarar su zuwa Ghana

Date:

Hukumar da ke kula da ƴan Najeriya a ƙasashen waje, NIDCOM ta ce ta ceto mata da ƙananan yara 58 daga hannun masu safarar mutane a Ghana.

Shugabar NDICOM, Abike Dabiri-Erewa ta ce wannan na zuwa ne bayan hukumar ta samu nasarar kuɓutar da wata yarinya ƴar mai shekara 15 zuwa 16 daga hannun masu neman yin safarar ta.

Sanarwar da kakakin hukumar, Abdur-Rahman Balogun ya fitar ta ce Abike Dabiri-Erewa ta samu labarin ceto ƴan Najeriyar daga Ghana ne a lokacin da ta kai ziyara domin ganin mutanen da aka yi safara zuwa birnin Accra na ƙasar Ghana.

Sanarwar ta ce daga cikin wadanda aka ceto akwai 47 ƴan asalin jihar Kano da biyar daga Katsina da biyu daga Jigawa da kuma huɗu daga jihar Kaduna.

Balogun ya bayyana cewa a cikin wata uku jimillar ƴan Najeriya 105 kenan da aka samu nasarar ceto su daga hannun masu safara a birnin Accra.

Hukumar ta ce, ta riga ta mayar da zangon farko na mutanen ceto zuwa gida Najeriya.

Ta kuma bayyana cewa, mafi yawan waɗanda ake safarar suna faɗawa tarko ne a bisa alƙawarin za a samar masu aiki a ƙasashen waje, wanda kuma hanya ce kawai ta yaudara ba gaskiya ba.

today daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp