fidelitybank

An ceto Ɗaliban Jami’ar Kogi 14 daga hannun ƴan ta’adda

Date:

Rundunar ‘yan sanda reshen jihar Kogi, ta tabbatar da ceto dalibai 14 na jami’ar Confluence University of Science and Technology, Osara, wadanda wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba suka yi garkuwa da su a ranar Alhamis, 9 ga watan Mayu, a lokacin da suke cikin harabar jami’ar da ke shirin yin jarrabawar kammala zangon farko.

Bayanin da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, SP William Ovye Aya ya samu ga DAILY POST ta hanyar sakon WhatsApp a ranar Lahadi, ya tabbatar da cewa jami’an tsaro na hadin gwiwa da aka gudanar sun ceto dalibai 14 tun bayan faruwar lamarin a ranar Alhamis.

Ya ce an garzaya da daliban da aka ceto zuwa asibiti domin samun agajin lafiya, yana mai jaddada cewa ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro a jihar za su ci gaba da tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi.

Tun da farko kwamishinan yada labarai da dabaru na jihar Kingsley Fanwo ya fitar da sanarwar ceto daliban daga hannun masu garkuwa da mutane.

Ya yaba da irin namijin kokarin da dukkan jami’an tsaro suka yi domin kubutar da daliban daga hannun wadanda suka yi garkuwa da su, inda ya ce ‘yan bindigar da ba a san ko su wanene ba sun fuskanci karfin tuwo wanda ya sa suka yi watsi da wadanda aka kashe.

nhgsfp

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp