fidelitybank

An cafke ƴan sanda biyu da suka ci zarafin wani mutum

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Ribas, ta cafke wasu jami’anta guda biyu da ke aiki a rundunar a kan wani faifan bidiyo da ke yaduwa a shafukan sada zumunta wanda ya kama su suna cin zarafin wani mutum mai suna Iyke a karamar hukumar Oyibo ta jihar.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Nwonyi Polycarp-Emeka, a wata sanarwa da ya fitar, ya yi tir da harin.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, CP, Grace Iringe-Koko, ta bayyana haka, inda ta ce a halin yanzu jami’an da abin ya shafa suna gaban kotu bisa laifin rashin da’ar da suka aikata, matakin da ya ce zai kawo cikas ga sauran jami’an ‘yan sanda.

Sanarwar ta kuma yi kira ga wanda abin ya shafa da ya fito ga sashin hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, domin bayar da bayaninsa tare da taimaka masa wajen kammala binciken, tare da tabbatar da cewa za’a kare sunan sa.

Ta ce: “Kwamishanan ‘yan sanda, CP Nwonyi Polycarp Emeka, ya yi Allah wadai da cin zarafin da ‘yan sanda suka yi wa wani mutum a wani faifan bidiyo da ke yawo a shafukan sada zumunta.

“An gano ’yan sandan da ke cikin bidiyon kuma an kama su. A yanzu haka suna hannun rundunar ‘yan sanda ana shari’a kan rashin da’ar da suka aikata wanda zai zama hana wasu ‘yan sanda katsalandan.

“Kwamishanan ‘yan sandan ya tabbatar wa da jama’a cewa za a binciki jami’an ‘yan sanda bisa wasu ka’idojin da suka shafi dabi’ar ‘yan sanda da kuma sanya takunkumin da ya dace.

“Rundunar ta kara tabbatar wa mutanen jihar Ribas nagartaccen kudirin ta na inganta bin doka da oda.”

Mutumin da ya kama lamarin, ya bayyana matakin da ‘yan sandan suka yi da irin aikin da rundunar ‘yan sandan da ke yaki da ‘yan fashi da makami ta rusa.

Ya kara da cewa irin wannan aika-aikar da ‘yan sanda ke yi ya sha faruwa a Oyigbo.

nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp