Rundunar ‘yan sandan jihar Ribas, ta cafke wasu jami’anta guda biyu da ke aiki a rundunar a kan wani faifan bidiyo da ke yaduwa a shafukan sada zumunta wanda ya kama su suna cin zarafin wani mutum mai suna Iyke a karamar hukumar Oyibo ta jihar.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Nwonyi Polycarp-Emeka, a wata sanarwa da ya fitar, ya yi tir da harin.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, CP, Grace Iringe-Koko, ta bayyana haka, inda ta ce a halin yanzu jami’an da abin ya shafa suna gaban kotu bisa laifin rashin da’ar da suka aikata, matakin da ya ce zai kawo cikas ga sauran jami’an ‘yan sanda.
Sanarwar ta kuma yi kira ga wanda abin ya shafa da ya fito ga sashin hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, domin bayar da bayaninsa tare da taimaka masa wajen kammala binciken, tare da tabbatar da cewa za’a kare sunan sa.
Ta ce: “Kwamishanan ‘yan sanda, CP Nwonyi Polycarp Emeka, ya yi Allah wadai da cin zarafin da ‘yan sanda suka yi wa wani mutum a wani faifan bidiyo da ke yawo a shafukan sada zumunta.
“An gano ’yan sandan da ke cikin bidiyon kuma an kama su. A yanzu haka suna hannun rundunar ‘yan sanda ana shari’a kan rashin da’ar da suka aikata wanda zai zama hana wasu ‘yan sanda katsalandan.
“Kwamishanan ‘yan sandan ya tabbatar wa da jama’a cewa za a binciki jami’an ‘yan sanda bisa wasu ka’idojin da suka shafi dabi’ar ‘yan sanda da kuma sanya takunkumin da ya dace.
“Rundunar ta kara tabbatar wa mutanen jihar Ribas nagartaccen kudirin ta na inganta bin doka da oda.”
Mutumin da ya kama lamarin, ya bayyana matakin da ‘yan sandan suka yi da irin aikin da rundunar ‘yan sandan da ke yaki da ‘yan fashi da makami ta rusa.
Ya kara da cewa irin wannan aika-aikar da ‘yan sanda ke yi ya sha faruwa a Oyigbo.