fidelitybank

An cafke ‘yan Shi’a 97 a Abuja tun bayan arangama da ‘Yan Sanda

Date:

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce ta kama ƴan shi’a 97 domin gurfanar da su gaban kotu, bayan wani rikici da ya barke tsakaninsu da ƴansanda a kasuwar Wuse da ke Abuja ranar Lahadi.

Rikicin da mabiya Sheikh Ibrahim El-Zakzaky ya yi sanadin mutuwar ‘yan sanda biyu, yayin da wasu uku suka samu munanan raunuka, da kuma lalata motocin ‘yan sanda guda uku da kungiyar ta Shi’ar ta yi.

A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ƴansanda, ACP Olumuyiwa Adejobi ya fitar a ranar Litinin ya bayyana cewa sahihan bayanan sirrin da suka samu ne ya bai wa jami’an ‘yan sanda damar kame wadanda ake zargin.

Ya kuma jaddada cewa Sufeto-Janar na ‘yan sanda, Kayode Egbetokun, ya bayar da umarnin a tsaurara matakan tsaro a kan lamarin.

Sufeto-Janar ɗin ya nanata kudurin ‘yan sanda na kame duk wadanda ke da hannu a rikicin tare da tabbatar da sun fuskanci shari’a.

Ya kuma sha alwashin hana duk wani nau’i na tarzoma a faɗin ƙasar, yana mai jaddada aniyar rundunar na tabbatar da doka da oda a fadin kasar.

Egbetokun ya yi Allah wadai da kisan gillar da ƴan shi’an suka yi wa jami’an ‘yan sandan, yana mai bayyana lamarin a matsayin abin takaici da rashin yarda.

Yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike, ‘yan sanda sun ƙuduri aniyar bankaɗo cikakken bayanin harin da kuma hana cin zarafin jami’an tsaro.

taraba news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp