fidelitybank

An cafke wanda ya kitsa harin Taraba

Date:

A wani gagarumin samame da suka kai, dakarun runduna ta 6 da Operation WHIRL STROKE (OPWS), sun kama ɗan ta’addan da ake zargi da kitsa harin da aka kai a ƙauyen Mararaban Azagawa da ke ƙaramar hukumar Bali a jihar Taraba.

Rundunar ta ce kamen ya biyo bayan harin da aka kai ranar 16 ga watan Yunin 2024, wanda ya yi sanadin asarar rayuka biyar da jikkata mutane da dama.

Muƙaddashin Daraktan hulda da jama’a na rundunar soji ta 6, Oni Olubodunde ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai.

A cewarsa, dakarun da ke sansanin ‘Forward Operating Base’ a ƙaramar hukumar Bali, sun ƙaddamar da wani samame na musamman bayan sahihan bayanan sirri da suka samu domin kamo waɗanda suka kai harin.

A yayin samamen ne sojojin suka kama wanda ake zargin shi ne ya kitsa harin mai suna Hassan Ibrahim wanda aka fi sani da Godu, ɗan shekara 39, kamar dai yadda sanarwar ta ce.

A yayin da ake kamen, sojojin sun ƙwato manyan makamai da harsasai, da kuma babur na ɗaya daga cikin waɗanda harin ya shafa.

Rundunar sojin ta ce wanda ake zargi ya amince cewa yana da hannu a harin kuma yana bayar da bayanai masu mahimmanci da za su kai ga kama sauran waɗanda ke da hannu a ciki.

A halin da ake ciki, kwamandan rundunar 6 Brigade Sector 3 OPWS, Birgediya Janar Kingsley Chidiebere Uwa, ya yaba wa jama’a bisa bayar da bayanai masu amfani da suka kai ga kama waɗannan mutane.

Ya kuma buƙaci jama’a da su ci gaba da mara wa jami’an tsaro wajen aikin kawar da masu aikata laifuka a jihar Taraba.

taraba news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp