Sojoji da dama ciki har da jami’an kabilar Zaghawa na shugaban kasar Chadi, Janar Mahamat Idris Deby aka kama a karshen mako bisa zargin kitsa juyin mulki.
Rahotanni sun ce yanzu haka ana tsare da su zuwa lokacin da jami’an hukumar leken asirin kasar za su kammala bincike.
Babu wata sanarwa a hukumance daga mahukunta a kan zargin kitsa juyin mulki, to amma bayanan hakan sun fito ne bayan da aka murkushe wasu ‘yan adawa a wata gwabzawa da aka yi tsakanin jami’an sojin da kuma ‘yan adawa a watan Oktoban da ya wuce.