fidelitybank

An cafke mutumin da ya kashe dansa ya kuma kona gawarsa

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Akwa Ibom ta ce, ta kama wani mutum da ake zargin ya kashe dan sa tare da kona gawarsa a kauyen Ebe Ikpe da ke karamar hukumar Essien Udim a jihar.

A cewar jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, SP Odiko Macdon, wanda ya zanta da manema labarai a ranar Talata, hakimin kauyen, Cif Akpan Aniekan, da shugaban karamar hukumar, Sylvester Akpan ne suka kai rahoton faruwar lamarin a hedikwatar ‘yan sanda ta Essien Udim. .

SP Macdon ya shaida wa manema labarai cewa: “Sun ruwaito cewa wani Innocent Uko na Ebe Ikpe ya yi amfani da adda wajen kashe dansa, Boniface Innocent Uko, mai shekaru 26, ya kona gawar sa, sannan ya jefar da gawarwakin a wani bayan gida da aka yi watsi da shi a cikin gidansa don boye lamarin.

“A bisa karfin rahoton, jami’an ‘yan sanda sun ziyarci wurin [sun gano] gawar da ta kone, yanzu an ajiye a dakin ajiye gawa. An kama wanda ake zargin, kuma ya amsa laifin kashe marigayin, bisa dalilan rashin da’a da cin zarafi da abin kunya.”

Kakakin ‘yan sandan ya kuma bayyana cewa rundunar ta kama Charley Edem John, wanda ake zargi da satar kananan yara biyu ‘yan shekara bakwai.

“Rundunar, bisa wani rahoto na sirri, ta kama Charley Edem John, wanda ya sace yara biyu, kowace shekara bakwai, daga makarantarsu. Wanda ake zargin ya yi amfani da dan uwansa, mai shekaru 10 kuma a makaranta daya, wajen fitar da yaran daga ajinsu,” in ji Macdon.

A cewar kakakin ‘yan sandan, za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kuliya da zarar an kammala bincike a kan su.

dailysun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp