fidelitybank

An cafke mutumin da ya baiwa matarsa guba domin ya gaji dukiyarta a Jigawa

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta cafke wani mutum mai suna Habu Ibrahim dan shekara 40 bisa zarginsa da baiwa matarsa guba a kauyen Danadama da ke karamar hukumar Sule Tankarkar.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, A T. Abdullahi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai.

Ya ce an kama wanda ake zargin ne bisa zarginsa da lakada abin sha da nama da guba, inda ya nufi matarsa mai suna Zakiya Uzairu mai shekaru 35 da nufin ya gaji dukiyarta.

Ya ce da samun rahoton, jami’an tsaro na sashen Sule Tankarkar sun yi gaggawar kama wanda ake zargin a wurin.

CP. Abdullahi ya ce an kawo wanda ake zargin ofishin ‘yan sanda shiyya da ke Sule Tankarkar domin yi masa tambayoyi, daga bisani kuma aka mika shi zuwa sashin binciken manyan laifuka na jiha (SCID) da ke Dutse don ci gaba da bincike.

“Lokacin da ake yi masa tambayoyi, wanda ake zargin ya yarda da aikata laifin, inda ya tabbatar da sahihancin bayanan da aka baiwa ‘yan sanda.

“Ya amince da niyyar kashe matarsa domin ya mallaki dabbobinta, da suka hada da awaki, tumaki, da shanu.

“Ya ce matar da kyar ta tsere bayan ta gane gubar kuma ta yi tunanin shirinsa,” in ji ‘yan sandan.

natforce 
latest news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp