fidelitybank

An cafke Mutumin da ake zargi da satar Yara biyar a Najeriya

Date:

Rundunar ‘yansanda ta jihar Akwa Ibom ta kama wani mutum bisa zargin satar wasu yara biyar ‘yan gida ɗaya.

Kwamishinan ‘yansandan jihar, Joseph Eribo ne ya bayyana haka, jiya Litinin, a lokacin gabatar da wanda ake zargi mai suna Promise Boniface, tare da wasu tarin waɗanda ake zargi da aikata miyagun laifuka da aka kama.

Jaridar Vanguard ta ruwaito an kama mutumin ne wanda ake zargin ya sato yaran daga wani gida a ƙaramar hukumar Obio Ibiono, bayan da haɗakar ‘yan sanda da mutanen ƙauyen suka yi farautarsa.

‘Yansanda sun ce da ana bincikensa Boniface ya ce ya samu yaran ne suna gararamba sun rasa na yi a cikin ruwan sama sai ya ɗauke su.

To amma kuma da aka matsa da bincikensa sai ya yarda cewa sato su ya yi, amma ya ce yanayin ayuwa ne ya sa shi haka, kuma wannan shi ne karon farko da ya taɓa yi.

Kwamishinan ‘yansandan ya ce tuni an damƙa yaran ga iyayensu cikin ƙoshin lafiya, kuma bayana kammala bincike za a gurfanar da mutumin d ake zargi da satar a gaban kotu.

nasarawa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp