Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa, ta cafke wasu gungun ‘yan fashi da makami da ke addabar jihar da kewaye.
Kakakin rundunar ‘yan sandan, DSP Lawan Shiisu Adam ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai.
Ya ce kama shi ya biyo bayan umarnin da Kwamishinan ‘yan sandan ya bayar na kai farmakin bakar fata da maboyar miyagun a fadin rundunar.
A cewarsa “Tawagar ‘yan sanda a ranar Juma’a karkashin jagorancin jami’in ‘yan sanda reshen Ringim Dibision, tare da gudanar da bincike mai inganci da sahihan bayanai na cewa wasu ‘yan fashi da makami sun kammala shirin fara wani mummunan farmaki a kan titin Wudil/Garko da ke karkashin jihar Kano.”
‘Yan sanda tare da taimakon ‘yan banga na yankin sun yi nasarar cafke wani matashi mai shekaru 22, Hamza Abdullahi da Hassan Ya’u mai shekaru 25 a hannunsu da wata karamar bindiga kirar bogi.”
DSP Adam ya ce, binciken da hukumar SCID ta gudanar ya kai ga kwato Babura biyu da bindigar gida guda daya.
Ya ce wadanda ake zargin sun amsa laifin aikata fashi da makami a kan titin Gujungu/Miga, titin Kiyawa/Shuwarin, da Fanisau/Kano duk a jihar Jigawa.
Za a gurfanar da duk wadanda ake tuhuma a gaban kotu bayan kammala bincike.