fidelitybank

An cafke mutanen da suka addabi Jigawa

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa, ta cafke wasu gungun ‘yan fashi da makami da ke addabar jihar da kewaye.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, DSP Lawan Shiisu Adam ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai.

Ya ce kama shi ya biyo bayan umarnin da Kwamishinan ‘yan sandan ya bayar na kai farmakin bakar fata da maboyar miyagun a fadin rundunar.

A cewarsa “Tawagar ‘yan sanda a ranar Juma’a karkashin jagorancin jami’in ‘yan sanda reshen Ringim Dibision, tare da gudanar da bincike mai inganci da sahihan bayanai na cewa wasu ‘yan fashi da makami sun kammala shirin fara wani mummunan farmaki a kan titin Wudil/Garko da ke karkashin jihar Kano.”

‘Yan sanda tare da taimakon ‘yan banga na yankin sun yi nasarar cafke wani matashi mai shekaru 22, Hamza Abdullahi da Hassan Ya’u mai shekaru 25 a hannunsu da wata karamar bindiga kirar bogi.”

DSP Adam ya ce, binciken da hukumar SCID ta gudanar ya kai ga kwato Babura biyu da bindigar gida guda daya.

Ya ce wadanda ake zargin sun amsa laifin aikata fashi da makami a kan titin Gujungu/Miga, titin Kiyawa/Shuwarin, da Fanisau/Kano duk a jihar Jigawa.

Za a gurfanar da duk wadanda ake tuhuma a gaban kotu bayan kammala bincike.

www.leadership ng.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp