Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce, ta kama mata da kuma wasu mutum biyu da ke da alaƙa da mutumin da ake zargi da yunkurin kai harin ta’addanci a filin taron Maulidin mabiya Ɗarikar Tijjaniya a makon da ya gabata.
Kwamishinan ƴan sandan jihar CP Salman Dogo ya ce mutumin da ya kitsa kai harin, Ahmad Adam Abba ɗan asalin ƙasar Chadi ne, kuma ya tsere zuwa ƙasar Kamaru amman suna ci gaba da bincike domin kamo shi.
Da yake gana wa da manema labarai, kwamishinan ƴan sandan ya bayyana cewa bayanan sirrin da suka samu a ranar 24 ga wannan watan, ya sa suka gano wasu na kokarin kai hari filin taron maulidi, har ma aka fitar da sanarwa cewa jama’a su yi hattara.
CP Salman ya kuma ce sun ƙwato wasu abubuwan fashewa, inda ya ƙara da cewa wanda ake zargin kafin zuwansa Kano ya kashe mutum goma 17 a Chadin kuma mutumin na shirye-shiryen kafa sansanin ƴan ta’adda a jihar.