fidelitybank

An cafke mutane uku da ake zargi da yin fashi da makami

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Edo ta ce, ta kama wasu mutane uku da ake zargin ‘yan fashi da makami ne da kuma ‘yan kungiyar asiri mai suna Eiye a garin Benin, babban birnin jihar.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, SP Chidi Nwabuzor ne ya bayyana hakan a ranar Litinin.

A cewarsa, “’yan fashi da makami uku da kuma ‘yan kungiyar Eiye Secret Cult Confraternity sun shiga hannun jami’an rundunar yaki da fashi da makami na hedikwatar ‘yan sanda ta Ugbekun, Benin ranar Lahadi.”

Ya ce ‘yan sandan sun kai farmaki wani Otal da ke kan hanyar Enomayo, Off Upper Sakponba Road, Benin, inda suka kama wani Bright Omonowa Clifford Patrick, da Isaac Peter tare da kwato bindiga guda daya da aka kera a gida da kuma Black Beret na Eiye Secret Cult Confraternity.

Ya ce an kama su ne biyo bayan samun sahihan bayanan sirri kan taron sirri da wadanda ake zargin suka yi a otal din.

PPRO ta yi nuni da cewa Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Mohammed Dankwara, ya gargadi ‘yan kungiyar asiri daban-daban da masu daukar nauyinsu da su daina ayyukan da suke yi a jihar ko kuma su fuskanci fushin doka.

nhgsfp

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...
X whatsapp