fidelitybank

An cafke mutane uku da ake zargi da yin fashi da makami

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Edo ta ce, ta kama wasu mutane uku da ake zargin ‘yan fashi da makami ne da kuma ‘yan kungiyar asiri mai suna Eiye a garin Benin, babban birnin jihar.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, SP Chidi Nwabuzor ne ya bayyana hakan a ranar Litinin.

A cewarsa, “’yan fashi da makami uku da kuma ‘yan kungiyar Eiye Secret Cult Confraternity sun shiga hannun jami’an rundunar yaki da fashi da makami na hedikwatar ‘yan sanda ta Ugbekun, Benin ranar Lahadi.”

Ya ce ‘yan sandan sun kai farmaki wani Otal da ke kan hanyar Enomayo, Off Upper Sakponba Road, Benin, inda suka kama wani Bright Omonowa Clifford Patrick, da Isaac Peter tare da kwato bindiga guda daya da aka kera a gida da kuma Black Beret na Eiye Secret Cult Confraternity.

Ya ce an kama su ne biyo bayan samun sahihan bayanan sirri kan taron sirri da wadanda ake zargin suka yi a otal din.

PPRO ta yi nuni da cewa Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Mohammed Dankwara, ya gargadi ‘yan kungiyar asiri daban-daban da masu daukar nauyinsu da su daina ayyukan da suke yi a jihar ko kuma su fuskanci fushin doka.

www.nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp