fidelitybank

An cafke mutane biyu da yunkurin haifar da rikici a zaben Edo

Date:

Rundunar ‘yansandan Najeriya ta ce, ta kama wasu mutum biyu da taje zargi da yunƙurin haifar da tarzoma a za ben gwamnan jihar Edo da ke gudanar a yau Asabar.

Cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yansandan ƙasar, ACP Olumuyiwa Adejobi, ya fitar ranar Asabar, ya ce ‘yansandan sun kama mutanen biyu masu shekara 43 da 41 ranar Juma’a da maraice bayan da suka samu bayanan sirri cewa mutanen na shirin tayar da tarzoma a zaɓen na yau.

ACP Adejobi ya ce an kama su ne a mazaɓar Oredo, inda kuma bayan fara bincikarsu aka gano ƙananan bindigogin pistol ƙirar gida guda uku da wata babba guda ita ma ƙirar gida.

Ya ƙara da cewa ‘yansanda na ci gaba da riƙe mutanen biyu domin faɗaɗa bincike, inda ya ce za a gurfanar da su a gaban kotu da zarar an kammala bincike.

A yau ne dai al’ummar jihar Edo ke gudanar da zaɓen gwaman jihar.

Tuni dai dama rundunar ‘yansandan ƙasar ta ce ta girke jamai’ai kusan 35,000 domin tabbatar da zaman lafiya a lokaci da bayan gudanar da zaɓen.

ng news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp