fidelitybank

An cafke mutane biyu da yunkurin haifar da rikici a zaben Edo

Date:

Rundunar ‘yansandan Najeriya ta ce, ta kama wasu mutum biyu da taje zargi da yunƙurin haifar da tarzoma a za ben gwamnan jihar Edo da ke gudanar a yau Asabar.

Cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yansandan ƙasar, ACP Olumuyiwa Adejobi, ya fitar ranar Asabar, ya ce ‘yansandan sun kama mutanen biyu masu shekara 43 da 41 ranar Juma’a da maraice bayan da suka samu bayanan sirri cewa mutanen na shirin tayar da tarzoma a zaɓen na yau.

ACP Adejobi ya ce an kama su ne a mazaɓar Oredo, inda kuma bayan fara bincikarsu aka gano ƙananan bindigogin pistol ƙirar gida guda uku da wata babba guda ita ma ƙirar gida.

Ya ƙara da cewa ‘yansanda na ci gaba da riƙe mutanen biyu domin faɗaɗa bincike, inda ya ce za a gurfanar da su a gaban kotu da zarar an kammala bincike.

A yau ne dai al’ummar jihar Edo ke gudanar da zaɓen gwaman jihar.

Tuni dai dama rundunar ‘yansandan ƙasar ta ce ta girke jamai’ai kusan 35,000 domin tabbatar da zaman lafiya a lokaci da bayan gudanar da zaɓen.

naija news legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp