fidelitybank

An cafke mutane 30 da aikata laifuka a Yobe

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Yobe, ta ce, tare da hadin gwiwar ‘yan uwa jami’an tsaro sun cafke mutane 30 da ake zargi da aikata laifuka a fadin jihar.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, DSP Dungus Abdulkarim ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Damaturu.

A cewarsa, daga cikin wadanda aka kama akwai Mohammed Garba mai shekaru 25 da kuma Ibrahim Mohammed mai shekaru 22 bisa zargin kashe wani mutum da suka shiga gidansa da laifin sata.

“Rundunar ta na jajantawa iyalan mamacin tare da tabbatar wa al’umma hukuncin da ya dace kan masu laifin.

“Duk da haka, yawancin masu laifin da aka kama sun yi zaman gidan yari a baya daga irin wannan laifuka”, in ji shi.

Ya kuma bayyana cewa abubuwan da aka kwato daga hannun wadanda ake zargin sun hada da: wuka da wayoyin hannu guda biyar na nau’ukan iri daban-daban.

“A halin da ake ciki, tun daga lokacin da aka fara gudanar da bincike na musamman don gurfanar da shi a gaban kotu domin hukumar ta bukaci nagartattun mutanen al’umma da su tallafa wa jami’an tsaro ta hanyar samar da bayanai masu amfani na duk wani yunkuri da ake zargi da kuma maboyar masu laifi,” in ji shi.

@nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp