fidelitybank

An cafke mutane 18 da aikata laifi a Kano

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano, ta kama mutane 18 da ake zargi ake zargi da kai hari ga mutanen da ba su ji ba ba su gani ba a kan titunan jihar nan.

Kwamishinan ‘yan sandan, Usaini Muhammad Gumel ne ya bayyana haka a wata hira da manema labarai da ya yi a ranar Litinin.

A cewarsa, an kama mutanen ne a wasu wuraren da aka gano a maboyar masu aikata laifuka a cikin birnin jihar nan.

Ya ce, rundunar ta samu nasarar kama su ne a yankunan Mazaunar Tanko da Dandishe da Kofar Dan Agundi da Kofar Mata da kuma Filin Idi.

Sauran sun hada da Kofar Na’Isa da Kwanar Diso da Kukar Bulukiya tare da Dorayi Babba.

Kwamishinan ya kuma ce, abubuwan da aka kwato daga hannun wadanda ake zargin sun hada da muggan makamai da kuma tabar wiwi.

Gumel ya kara da cewa duk wadanda ake zargin za a tantance su yadda ya kamata, kuma bayan kammala bincike za a gurfanar da su a gaban kotu.

 

leadership news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp