fidelitybank

An cafke mutane 15 ‘yan kungiyar da suka addabi Adamawa da sace-sace

Date:

Jami’an ‘yan sanda a jihar Adamawa sun kama wasu matasa 15 na wata kungiya mai suna Shila Boys, wadanda suka kware wajen kwace wayoyi da sauran kayayyaki daga mazauna garin.

Rundunar ‘yan sandan jihar, wacce ta sanar da kamun na baya-bayan nan ta wata sanarwa mai dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na ‘yan sandan, Suleiman Nguroje, ta ce an gano wayoyin hannu guda tara da injin POS da muggan makamai da kuma muggan kwayoyi.

Sanarwar ta ambaci sunayen wadanda ake zargin kamar haka: Abdullahi Shuaibu, 18; Auwal Saleh, 18; Usman Abdullahi, 21; Auwal Isah, 20; Usman Ahmadu, 32; Muhammad Abubakar, 18; da Jamilu Hassan, 19.

Sauran su ne Abdulsalam Abdullahi mai shekaru 20; Salisu Umar, 19; Yahaya Umaru, 25; Salahudeen Auwal,18; Yusuf Ahmed, mai shekaru 20; Jamilu Sani, 18; Abraham Joel, 18; da Muhammad Auwal, 19.

Rundunar ‘yan sandan ta ce an kama wadanda ake zargin ne a daidai lokacin da aka kammala bikin Sallah a garin Yola da ke karamar hukumar Yola ta Kudu, da Jimeta a karamar hukumar Yola ta Arewa da kuma kewaye.

“Kwamishanan ‘yan sandan jihar, CP Dankombo Morris, ya yabawa mutanen jihar Adamawa bisa hadin kan da suke bayarwa wajen yaki da fashi da makami, fasa gidaje da kuma munanan laifuka na kungiyar asiri ta ‘Shila’,” in ji sanarwar ta ‘yan sandan.

newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp