fidelitybank

An cafke mutane 15 ‘yan kungiyar da suka addabi Adamawa da sace-sace

Date:

Jami’an ‘yan sanda a jihar Adamawa sun kama wasu matasa 15 na wata kungiya mai suna Shila Boys, wadanda suka kware wajen kwace wayoyi da sauran kayayyaki daga mazauna garin.

Rundunar ‘yan sandan jihar, wacce ta sanar da kamun na baya-bayan nan ta wata sanarwa mai dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na ‘yan sandan, Suleiman Nguroje, ta ce an gano wayoyin hannu guda tara da injin POS da muggan makamai da kuma muggan kwayoyi.

Sanarwar ta ambaci sunayen wadanda ake zargin kamar haka: Abdullahi Shuaibu, 18; Auwal Saleh, 18; Usman Abdullahi, 21; Auwal Isah, 20; Usman Ahmadu, 32; Muhammad Abubakar, 18; da Jamilu Hassan, 19.

Sauran su ne Abdulsalam Abdullahi mai shekaru 20; Salisu Umar, 19; Yahaya Umaru, 25; Salahudeen Auwal,18; Yusuf Ahmed, mai shekaru 20; Jamilu Sani, 18; Abraham Joel, 18; da Muhammad Auwal, 19.

Rundunar ‘yan sandan ta ce an kama wadanda ake zargin ne a daidai lokacin da aka kammala bikin Sallah a garin Yola da ke karamar hukumar Yola ta Kudu, da Jimeta a karamar hukumar Yola ta Arewa da kuma kewaye.

“Kwamishanan ‘yan sandan jihar, CP Dankombo Morris, ya yabawa mutanen jihar Adamawa bisa hadin kan da suke bayarwa wajen yaki da fashi da makami, fasa gidaje da kuma munanan laifuka na kungiyar asiri ta ‘Shila’,” in ji sanarwar ta ‘yan sandan.

fg spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp