fidelitybank

An cafke mutane 100 da shirya auren Luwadi a Delta

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Delta ta bayyana cewa, ta kama wasu matasa fiye da 100 bisa zargin su da shirya shagulgulan auren ‘yan luwaɗi da maɗigo a wani otal.

Rundunar ta bayyana hakan ne a wani saƙo da ta wallafa a shafinta na X (Twitter), kuma ta ce nan ba da daɗewa ba za ta gurfanar da wadanda ake zargin a kotu.

Rahotanni sun nuna cewa tun bayan sanya hannu kan dokar hana luwaɗi da maɗigo a shekarar 2014, jami’an tsaro sun kama mutanen da ake kyautata zaton ‘yan luwadi ne tare da gurfanar da su gaban shari’a.

A watan Disambar 2020, rundunar ‘yan sandan jihar Legas ta kama mutum 10 da ake zargi da aikata luwadi a wani gidan karuwai.

A shekarar 2018 kuma, ‘yan sanda sun kama wasu maza 57 bisa zargin yin luwadi a otal.

Haka zalika ma a watan Janairun 2022, an kama wasu mutane takwas da ake zargi su ma da yin luwadi da wani otal.

Rahotanni dai sun ce dokar hana luwadi a shekarar 2014 ta tanadi daurin shekara 14, ga duk wanda aka samu da laifin yin jima’i da jinsi ɗaya.

legit nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp