fidelitybank

An cafke Matsafa biyu da yunƙurin asirce shugaban ƙasa

Date:

Hukumomin Zambiya sun kama wasu mutum biyu da ake zargi ”matsafa” ne da aka bai wa aikin asirce shugaban ƙasar.

‘Yansanda sun ce sun kama Jasten Mabulesse Candunde da Leonard Phiri a Lusaka, babban birnin ƙasar.

“Aikin da suka ƙudiri aniyar yi shi ne amfani da layu wajen cutar da shugaba Hakainde Hichilema”, kamar yadda sanarwar ‘yansandan ta bayyana.

Mutane da dama a ƙasar da ke kudancin Afirka sun yi amanna da bokaye, inda a lokuta da dama mutane kan rayu da fargabar tsoron asiri.

‘Yansanda sun yi zargin cewa Nelson Banda – ƙanin wani ɗan majalisa Emmanuel Banda, da aka fi sani da “Jay Jay” Banda – ne ya bai wa bokayen aikin sabauta shugaban ƙasar.

A watan da ya gabata ne aka kama ɗan majalisar a makwabciyar ƙasar Zimbabwe kan zargin laifin fashi, zargin da ya musanta.

Sanarwar ‘yansanda ta ce wanda ake zargi da bai wa bokayen aikin ya tsere, inda suka alƙawarta farauto shi.

An dai kama bokayen ƙarƙashin dokokin tsafi na ƙasar, inda ake zarginsu da aikata tsafi da zaluntar dabbobin, bayan da ka same su da tarin guraye da layu da kuma hawainiya da ranta, kamar yadda ‘yansanda suka yi bayani. A cewar BBC.

Bokayen sun kuma bayyana wa ‘yansanda cewa an yi musu alƙawarin kuɗin ƙasar fiye da kwaca miliyan biyu kimanin dala 73,000, idan suka kammala aikin sabauta shugaban ƙasar.

vgn news today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp