Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa, ta cafke wani mutum mai suna Barnabas Abduneza mai shekaru 40 bisa zargin kashe karamar yarinya.
Wani mazaunin kauyen Kpasham da ke karamar hukumar Demsa a jihar Adamawa, Abduneza, ya kai wa mamacin da mahaifiyarta hari a makon jiya, 29 ga watan Satumba a kauyen Kadamti, lamarin da ya yi sanadin mutuwar karamar yarinya da kuma mummunar rauni a jikin mahaifiyar.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Sulaiman Nguroje, wanda ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya samu da safiyar Asabar, ya ce, “Bayan harin da aka kai wa wata mata da yaronta a kauyen Kadamti da ke karamar hukumar Numan a ranar 29/9/2022 da wanda ya yi sanadiyar mutuwar jaririn tare da raunata mahaifiyar, jami’an rundunar ‘yan sandan da ke yankin Numan Dibision, Ma’aikatan Operation Farauta da Samariya nagari suka fantsama tare da kama daya dangane da laifin.
“Wanda ake zargin, Barnabas Abduneza mai shekaru 40, mazaunin kauyen Kpasham, a karamar hukumar Demsa, an kama shi ne bayan wani sahihan bayanai.”