fidelitybank

An cafke matasa biyu a Kano da zargin kashe Budurwarsu ta hanyar zubar da ciki

Date:

Rundunar ƴan sanda a jihar Kano, ta tabbatar da gano gawar wata matashiya ƴar shekara 20 ɗauke da juna biyu yashe a gefen titi a ƙauyen Anadariya da ke ƙaramar hukumar Bebeji.

Cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook, kakakin rundunar ƴan sandan jihar, Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce an kama mutum biyu da ake zargi da tafka aika-aikar.

Ya ce kamen ya faru ne sakamakon rahoton da mazauna yankin suka shigar lamarin da ya sa kwamishinan ƴan sandan jihar, Mamman Dauda ya tura jami’ansa zuwa inda lamarin ya faru.

Kakakin rundunar ya bayyana sunan matashiyar da Theresa Yakubu inda ya ce mutanen da ake zargi da kashe ta saurayinta ne da kuma abokinsa.

Saurayin marigayiyar ya amsa aikata laifin inda ya ce shi ya ƙunsa mata ciki kuma ya hada baki da abokinsa su kashe ta bayan da duk wani yunƙuri na zubar da jaririn cikin ya ci tura.

A nasa ɓangaren, kwamishinan ƴan sandan ya miƙa ta’aziyya ga iyalan marigayiyar inda kuma ya bai wa al’ummar yankin tabbacin cewa za su yi duk mai yiwuwa domin tabbatar da adalci.

Ya kuma nemi mazauna unguwar su taimaka da bayanan da za su kai ga cafke sauran mutanen da ke da hannu a lamarin.

vanguard (nigeria)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...
X whatsapp