fidelitybank

An cafke masu garkuwa da mutane a Abuja

Date:

Rundunar ƴan sandan Abuja ta kama wasu gawurtattun masu garkuwa biyar a yankunan Gwagwa da Dei-Dei bayan samamen da jami’an rundunar suka kai kan maɓoyar su tsawon yini biyu.

Mai magana da yawun rundunar, SP Josephine Adeh cikin wata sanarwa da ta fitar ta ce jami’an rundunar sun kai samamen tsakanin 30 ga watan Yuni da kuma 3 ga watan Yuli bayan samun bayanan sirri.

Mutanen da aka kama su biyar da shekarunsu tsakanin 20 zuwa 29, ana zarginsu da hannu da sace wasu mutane a Gwagwa ranar 12 ga watan Yuni inda suka karɓi kuɗin fansa naira miliyan 12 daga wajen iyalansu inda kuma suka kashe mutum biyu.

Ana kuma zargin mutanen da aka kama da sace-sacen mutane da aikata miyagun laifuka a sassan babban birnin Najeriyar.

Rundunar ta ce an ƙwace bindiga huɗu ƙirar AK47 da alburusai a hannun mutanen bayan da suka tabbatar da miyagun ayyukan da suka aikatawa.

Yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike kan mutanen, kwamishinan ƴan sandan Abuja, Benneth Igweh ya nanata ƙudirin rundunar na tabbatar da tsaron al’ummar birnin.

vanguard news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp