fidelitybank

An cafke masu garkuwa da mutane a Abuja

Date:

Rundunar ƴansanda a babban birnin Najeriya, Abuja ta ce, ta kai farmaki kan wata moɓoyar wasu mutane da ake zargi da satar mutane domin karɓar kuɗin fansa a birnin.

Ƴansandan sun ce sun kai farmakin ne bayan samun bayanan sirri, abin da ya sa suka yi wa ƴanbindigar kwanton ɓauna a sansanoninsu a dajin Kwati da ke yankin jihar Kaduna.

Inda suka yi nasarar kama hudu daga cikin waɗanda ake zargin, sannan suka kuɓutar da wasu mutanen da ake garkuwa da su.

Mai magana da yawun rundunar ƴansandan ta Abuja, Josephine Adeh ta ce sun kai samamen ne tare da taimakon jami’an DSS da sojoji da kuma ƴanfarauta.

Ta kuma ƙara da cewa sun kama bindigogi a lokacin samamen.

Matsalar satar mutane domin karɓar kuɗin fansa ta fara yawaita a Abuja, inda a baya-bayan nan aka kama wasu ƴangida ɗaya a yankin Bwari, inda har ta kai ga kashe ɗaya daga cikinsu.

nigeria legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp