fidelitybank

An cafke Manajan jirgin ruwan da ya kife ya kashe mutane 21 a Legas

Date:

An kama manajan wani jirgin ruwan da ya kife ranar Litinin a jihar Legas, bisa zarginsa da yin sakaci da rashin bin ka’idojin tsaro.

Shugabar hukumar kula da hanyoyin ruwa ta kasa a yankin Legas, NIWA, Misis Sarat Braimah, ta bayyana hakan a wata sanarwa da ta fitar ranar Talata a Legas.

Ta ce an kama shi ne sakamakon wani bincike da aka yi dalla dalla kan lamarin.

“An kama shi ne da nufin tabbatar da bin diddigi da kuma kafa misali mai tsauri na bin ka’idojin hanyoyin ruwa don hana afkuwar lamarin nan gaba. Ana ci gaba da gudanar da wasu matakai na shari’a yayin da ake ci gaba da bincike,” inji ta.

A cewarta, dole ne ma’aikacin jirgin ya fito da kyaftin din jirgin, yana mai jaddada cewa, an tabbatar da cewa jirgin ruwan fiber ya kauce daga tasharsa, ya kuma yi karo da wani jirgin ruwan katako saboda cikas da kyaftin din.

Braimah ya ce wannan cikas ya samo asali ne saboda lodin da ke cikin jirgin ruwan fiber, yana mai cewa jirgin mallakar Only God Ferry ya gaza bin ka’idojin tsaro da kuma hanyoyin zirga-zirgar ababen hawa.

the nation newspaper 
today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp