Jami’an tsaron Habasha sun ce sun kama sama da mutum 12 da ake zargi da tsara kai hari kan shugabanni da ‘yanjaridar da ke halartar taron ƙungiyar hadin kan ƙasashen Afirka ta African Union a ƙasar.
Gidan talabijin na Ethio Forum ya ruwaito cewa “ana yunƙurin kai wa wasu shugabannin Afirka hari domin kashe su a Addis Ababa, amma har an kai ƙara gaban kotu”.
Jerin sunayen da aka kai gaban kotun ya nuna mutum 15 da ake zargi, ciki har da wani jami’i a ɓangaren ‘yan’adawar ƙasar da ake zargi da karɓar aiki daga wata ƙungiya mai suna Fano domin kashe mahalarta taron.
“An kama mutanen da sunayensu ke sama ne a ranar 13 ga watan Fabraoiru yayin da suke yunƙurin kai harin ta’addanci yayin taron AU,” kamar yadda takardun na ‘yansanda suka bayyana.