fidelitybank

An cafke Barawon da ake zargi da dauke Tirelar mota dauke da tan 35 na kwaya

Date:

Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi sun kama wani da ake zargin dan fashi ne da ya yi awon gaba da wata motar tirela dauke da tan 35 na man gyada wanda kudinsa ya kai kusan Naira miliyan 30.

Rundunar ‘yan sandan ta ce hedikwatar ‘yan sanda ta Toro ta samu kiran gaggawa game da satar motar da aka yi a tashar tirela ta Maraban Jos a jihar Kaduna a ranar 12 ga Afrilu, 2024.

Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Bauchi, SP Ahmed Wakil, a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi, ya ce motar da aka sace, kirar DAF CF 85, ta fito ne daga Umuahia da ke Jihar Abia, ta nufi Jihar Kano a lokacin da aka sace ta a Jihar Kaduna.

Sanarwar ta ce, binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa direban motar ya tsaya a kusa da tashar tirela ta Maraban Jos domin yin wanka sai daga baya ya dawo ya gano cewa tirelar ta bace daga inda aka ajiye ta.

Sanarwar ta kuma kara da cewa kwamishinan ‘yan sandan jihar Bauchi, CP Auwal Muhammad, ya bayar da umarnin gudanar da bincike na gaskiya da hukumar binciken manyan laifuka ta jihar (SCID) kan satar motar.

Rundunar ‘yan sandan ta ce za a gurfanar da wanda ake zargin zuwa kotu da zarar an kammala bincike kan lamarin.

daily post today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...

Shugaban Laberiya ya je ta’aziyyar Buhari a Monrovia

Shugaban Ƙsaar Laberiya Joseph Nyuma Boakai ya kai ziyarar...

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...

Iran ta zartar da hukuncin kisa a kan Mutane 3

Hukumomi a Iran sun zartar wa mutum uku hukuncin...

Ƴansanda sun kama ƙasurgumin ɗanbindiga a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna ta ce, jami'an ta sun...

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...
X whatsapp