fidelitybank

An cafke Barawon da ake zargi da dauke Tirelar mota dauke da tan 35 na kwaya

Date:

Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi sun kama wani da ake zargin dan fashi ne da ya yi awon gaba da wata motar tirela dauke da tan 35 na man gyada wanda kudinsa ya kai kusan Naira miliyan 30.

Rundunar ‘yan sandan ta ce hedikwatar ‘yan sanda ta Toro ta samu kiran gaggawa game da satar motar da aka yi a tashar tirela ta Maraban Jos a jihar Kaduna a ranar 12 ga Afrilu, 2024.

Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Bauchi, SP Ahmed Wakil, a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi, ya ce motar da aka sace, kirar DAF CF 85, ta fito ne daga Umuahia da ke Jihar Abia, ta nufi Jihar Kano a lokacin da aka sace ta a Jihar Kaduna.

Sanarwar ta ce, binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa direban motar ya tsaya a kusa da tashar tirela ta Maraban Jos domin yin wanka sai daga baya ya dawo ya gano cewa tirelar ta bace daga inda aka ajiye ta.

Sanarwar ta kuma kara da cewa kwamishinan ‘yan sandan jihar Bauchi, CP Auwal Muhammad, ya bayar da umarnin gudanar da bincike na gaskiya da hukumar binciken manyan laifuka ta jihar (SCID) kan satar motar.

Rundunar ‘yan sandan ta ce za a gurfanar da wanda ake zargin zuwa kotu da zarar an kammala bincike kan lamarin.

nigerian 
newspapers today the sun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp