Shugaban Hukumar Zaɓe ta INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, ya ayyana buɗe zauren karɓar sakamakon zaɓen shugaban ƙasa na 2023 a hukumance.
Shugaban na INEC ya ce za a fara tattara sakamakon ne daga gundumomi zuwa ƙananan hukumomi, daga nan sai a kai matakin jiha.
Ya ce bayan nan ne kuma za a kai sakamakon zuwa Abuja, babban birnin tarayya, a zauren tattara sakamakon.
Yakubu ya ce baturen zaɓe idan ya zo sanar da sakamakon zaɓen jihar da ya zo da ita, zai faɗi ta yadda kowa zai ji, inda zai faɗi yawan mutanen da aka yi wa rajista da waɗanda suka samu damar kaɗa kuri’a da kuma kuri’un da suka ɓaci.
Karanta Wannan: Da Dumi-Dumi: An kona ofishin INEC na Takai a Kano
Shugaban na INEC ya ce bayan haka baturen tattara sakamakon zaɓen kowace jiha zai faɗi yawan kuri’un da kowace jam’iyya ta samu, sannan sai a kira wakilan jam’iyya su zo su sanya hannu idan suka amince da sakamakon.
Shugaban na INEC ya yi kira ga dukkan wakilan jam’iyyu da kuma ‘yan jarida da su tabbatar da cewa sakamakon zaɓen da hukumar ta sanar kaɗai za su yaɗa.
Ya ƙara da cewa babu wani wuri da ake sanar da sakamakon zaɓen illa babban zauren da aka tanada.
Yanzu dai an tafi hutun har zuwa karfe shida na yamma lokacin da za a dawo domin fara sanar da sakamakon zaɓen shugaban ƙasar gadan-gadan.