Wasu ‘yan bindiga sun kai wa tawagar jami’an hukumar kiyaye haddura ta kasa FRSC hari da suka hada da wani jami’i, direba, da wasu ma’aikata biyu a jihar Anambra.
A yayin harin da aka kai ranar Lahadi a kan hanyar Igbo-Uku-Uga a jihar, maharan sun kashe mutane biyu tare da jikkata daya.
Rundunar dai na gudanar da aikin sintiri na yau da kullum a yankin ne ‘yan bindigar suka bude musu wuta, inda suka kashe jami’an, gawar guda biyu yayin da daya kuma ya tsere cikin daji.
An garzaya da shugaban tawagar wanda ya samu munanan raunuka zuwa asibiti.
A nasa martani, Shugaban Rundunar, Dakta Boboye Oyeyemi, ya yi tir da harin tare da jajantawa iyalan ma’aikatan da suka mutu.
Ya kuma jajantawa kwamandan runduna da ma’aikatan rundunar FRSC ta Igbo-Uku, da ma daukacin jami’an hukumar da ma’aikatan hukumar bisa wannan rashi.
Oyeyemi ya tabbatar musu da cewa tuni rundunar ta fara aiki tare da rundunar ‘yan sandan Najeriya da sauran jami’an tsaro da abin ya shafa, domin ganin an kama wadanda suka aikata wannan aika-aika tare da basu damar fuskantar cikakken tsarin doka.