Wasu gungun mutane sun bankawa wani da ake zargin dan fashi da makami wuta a kan titin Bazunu, kofar kasuwar Igbudu, Warri, jihar Delta, a daren ranar Alhamis.
Rahottani na cewa lamarin ya faru ne yayin da wata mata ta yi awon gaba da kayanta a kan hanyarta ta daga kasuwa da misalin karfe 9 na dare.
An ce ’yan bangar su uku sun kai farmaki yankin ne a cikin babur mai uku na kasuwanci inda suka daba wa matar wuka bayan sun kwace mata kayanta.
Sai dai kukan da ta yi na neman agaji ya sanar da masu wucewa da mazauna yankin da sauran ‘yan kasuwa, inda suka kori barayin. An kama daya daga cikinsu yayin da sauran biyun suka tsere.
An yi masa dukan tsiya kafin a kone shi.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Delta, DSP Bright Edafe, bai amsa kiran wayarsa ba ko kuma amsa sakonnin tes da aka aika masa domin jin ta bakinsa.