fidelitybank

An bankado Cocin da ya koma masana’antar Jarirai a Imo

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Imo, ta gano wani coci da ake amfani da shi a matsayin masana’antar jarirai a kan hanyar MCC/Uratta.

‘Yan sandan sun kai farmaki cocin Jesus Life Assembly ne a ranar Alhamis bayan da sashen dabara suka samu labarin wani dan kasa mai suna Amarachi Okechukwu Dioku.

Yarinyar mai shekaru 18 daga Umudurualaoka a cikin karamar hukumar Mbaitoli, iyayenta ne suka bayar da rahoton bacewar ta a ranar 23 ga Mayu 2021.

Karanta Wannan: Rashin tsaro a Imo ba laifin Gwamna ba ne – Marcellinus

Kwanan nan an ga matashin a harabar cocin, wanda ke wani waje da ke kusa da Lambun Makaranta a karamar hukumar Owerri ta Arewa.

Kwamishinan ‘yan sanda, Rabiu Hussaini, ya aike da sashin yaki da masu garkuwa da mutane domin kai samame wurin da aka gano babban wanda ake zargin Evangelist Ugochi Orisakwe mai shekaru 47.

An kama Ugochi ne tare da ‘yan kungiyar ta, Chidi Orisakwe, ‘yar shekara 34, Pauline Nwagbunwanne mai shekaru 42, Elizabeth Uzoma mai shekaru 61 da kuma Chibueze Joy mai shekaru 31.

An ceto Amarachi Dioku ba tare da jin rauni ba tare da dauke da juna biyu na wata biyar sannan aka kaita asibitin gwamnati domin yi mata magani daga nan aka sake haduwa da iyayenta.

A yayin da ake yi mata tambayoyi, Evangelist Ugochi ta amsa cewa ta kasance tana amfani da cocin a matsayin wurin da ake ajiye yara mata da kuma yi musu ciki.

Ta shaida wa jami’an ‘yan sanda cewa bayan an haihu, ana biyan ‘yan matan kuma ana sayar da jariransu ga masu kudi da marasa haihuwa.

“Ana ci gaba da gudanar da bincike kuma ana ci gaba da kokarin kama wasu ‘yan kungiyar da ke gudun hijira,” in ji rundunar ‘yan sandan jihar Imo.

vgn news today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp